Dakarun ‘Operation Forest Sanity’ sun kashe ‘yan bindiga biyu tare da tarwatasa sansaninsu a karamar hukumar Chikun da ke Jihar kdauna.
Wannan na cikin sanarwar da Kwamishinan Tsaron Cikin Gidan jihar, Samuel Aruwan, ya fitar, ta ce dakarun sun samu wannan nasarar ne, biyo bayan fafatawa da dakarun suka yi yayin da suke yin sintiri daura da dajin Kaboresha zuwa Rijana da ke a yankin Kuzo-Kujeni-Gwanto a karamar hukumar Kachia.
- ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3, Sun Raunata Wasu A Katsina
- CMG Ya Yi Bitar Shirin Murnar Bikin Bazara Na 2023 Karo Na Hudu
Sanarwar ta kara da cewa, dakarun sun kuma tarwatsa sansanan ‘yan bindiga guda takwas da ke a Kutura zuwa Rijan, inda hakan ya sa wasun suka tsere.
Dakrun sun kuma kwato babura uku da wasu kaya da dama ciki har da kakin sojoji daga hannun ‘yan bindigar.
Sanarwar, ta ce gwaman jihar, Nasir El-Rufai, ya yaba da kokarin dakarun suka yi kan wannan nasarar suka samu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp