ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojojin Sama Sun Hallaka Fiye da Ƴan Ta’adda 40 A Borno

by Abubakar Sulaiman
5 months ago
Sojoji

Rundunar Sojin Saman Nijeriya (NAF) ta tabbatar da kashe fiye da ƴan ta’adda 40 a hare-haren sama da aka ƙaddamar a yankunan Azir da Musarram na Jihar Borno, lamarin da ya tarwatsa shirye-shiryen hare-hare da suke shirin kai wa, tare da ƙarfafa aiyukan Sojojin ƙasa a yankin. Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Daraktan Hulɗa da jama’a na NAF, Air Commodore Ehimen Ejodame, ya fitar a ranar Lahadi a Abuja.

A cewar Ejodame, hare-haren sun gudana ne a ranakun 15 da 16 ga Janairu ta hannun ɓangaren Operation HAƊIN KAI, bayan samun sahihin bayanan sirri da kuma haɗin gwuiwa da Sojojin da ke artabu a fili. Ya ce da sassafe a ranar 16 ga Janairu, jiragen NAF sun amsa kiran gaggawa a Azir, inda Sojoji ke fafatawa da ƴan ta’addan da ke ƙoƙarin janyewa daga yankin.

 

ADVERTISEMENT

Bincike daga na’urar sama ya gano wasu daga cikin ƴan ta’addan suna ƙoƙarin sake taruwa a ƙarƙashin bishiyoyi a kusa, lamarin da ya sa aka ƙaddamar da jerin hare-haren saman da suka hallaka da dama daga cikinsu. Rahoton bayan harin ya tabbatar da cewa babu barazanar da ta yi saura, yayin da bayanai daga Sojoji, da hukumomin yankin da mazauna wurin suka nuna an samu kwanciyar hankali bayan raguwar ƴan ta’adda a yankin.

Tun a ranar 15 ga Janairu kuma, NAF ta kai harin sama a Musarram da ke yankin Tumbuns bayan samun bayanan sirrin cewa ƴan ta’adda na taruwa a kan jiragen ruwa domin kai hari a yankunan Baga da Fish Dam.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Jiragen sama sun hangi kusan kwale-kwale 10 ɗauke da fiye da ƴan ta’adda 40, inda aka tarwatsa su ta hanyar kai hare-hare ba’a ƙaƙƙautawa, Shugaban Sojin Sama, Air Marshal Sunday Aneke, ya jaddada aniyar NAF na ci gaba da ba da tallafin sama ga Sojojin ƙasa domin hana ƴan ta’adda samun damar sake farfaɗowa da tabbatar da tsaron yankunan da abin ya shafa.

Sojoji
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje
  • Abubakar Sulaiman
    Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Maniyyatan Nijeriya
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Next Post
Asiri Ya Tonu: Yadda Aka Kashe Uwa da Ƴaƴanta Shida A Kano

Asiri Ya Tonu: Yadda Aka Kashe Uwa da Ƴaƴanta Shida A Kano

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.