Tarayyar Turai (EU) ta yi watsi da cikakken aikin lura da zaɓen Nijeriya na 2027, tana mai cewa matsalar tsaro tana ƙara taɓarɓarewa kuma abin da suka kira rashin kyakkyawar mu’amala ga masu lura da zaɓe da jami’ansu bayan zaɓukan 2023.
Wannan mataki ta kawo ƙarshen jerin ayyukan lura da zaɓen da EU ta yi a Nijeriya na kusan shekaru fiye da ashirin.
EU ta bayyana matakin ne a matsayin amsa ga wata wasiƙa daga hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC), wadda ta gayyaci ƙungiyar don ta sa ido kan zaɓukan 2027.
A cikin martini kan wasiƙar, EU ta kawo dalilai biyu na yanke hukuncinta, na farko shi ne, taɓarɓarewar tsaro a duk faɗin ƙasar da kuma rashin kyakkyawar mu’amala da masu lura da jami’anta bayan fitar da rahoton ƙarshe game da zaɓen 2023.
Maimakon tura manyan jami’ai a lokacin zaɓen, EU ta ce za ta ajiye ƙananan jami’ai kaɗan a Abuja don sa ido kan abubuwan da ke faruwa kuma su ba da rahoto zuwa Brussels.
INEC ta rubuta wa EU tana neman masu aikin sa ido a 2027. Hukumar ta saba aika irin wannan gayyata kafin kowane zaɓen tun bayan dawowar mulkin farar hula a 1999.
EU ta sa ido kan zaɓen Nijeriya a shekarun 2003, 2007, 2011, 2015, 2019 da 2023. Babban mai sa ido, ɗan majalisar Turai na Ireland Barry Andrews, ya bayyana cewa sau 7 yana sa ido a zaɓen Nijeriya tun daga 1999.
A zaɓen 2023, wata tawagar ƙwararru 11 ta isa Abuja a ranar 11 ga Janairu, makonni shida kafin zaɓen shugaban ƙasa. Bayan haka, an tura masu sa ido a faɗin jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya.
Wani tawagar majalisar Turai ma ta shiga aikin sa ido don zaɓen shugaban ƙasa da na majalisar ƙasa. Tawagar ta tsaya a ƙasar har zuwa 11 ga Afrilu, makonni bayan zaɓukan shugaban ƙasa na ranar 25 ga Fabrairu da na gwamnonin jihohi na ranar 18 ga Maris. Tawagar ta gabatar da rahoton na ƙarshe a Abuja a watan Yuni, 2023.
Rahoton ya ƙunshi shawarwari 25 a faɗin manyan yankuna guda shida. Ya gano abin da ya bayyana a matsayin rauni masu ɗorewa a tsarin zaɓe. Ya ce gazawar a dokar zaɓe da gudanarwa sun hana gudanar da zaɓuka masu kyau da kuma sun lalata amincewar jama’a da INEC.
Sakamakon binciken ya haifar da zanga-zanga a ofishin jakadancin EU a Abuja, inda masu shirya zanga-zangar suka zargi ƙungiyar da tsoma baki a harkokin cikin gudanwa a Nijeriya kuma suna neman a janye rahoton.
Wasu ƴan adawa da ƙungiyoyin farar hula sunn cewa magoya bayan jam’iyyar APC ne suka ɗauki nauyin zanga-zangar. An musanta wannan zargi.
Matakin EU ta zo ne a yayin da ake fuskantar tashin hankali a wasu sassan arewa maso yamma da arewa maso gabas da arewa ta tsakiya da kudu maso gabas, inda hana fita da hare-hare kan wuraren zaɓe suka kawo cikas ga zaɓen 2023 a wasu jihohi.
Harkokin sanya idanu kan zaɓe na buƙatar masu sa ido su tafi wuraren kaɗa ƙuri’a a ƙauyuka da wurare masu nisa, sau da yawa ba tare da isasshen tallafin tsaro ba, wanda ke sanya aikin tura su ya zama mai wahala sosai.
Ana kuma sa ran wannan mataki zai tasiri ga kulawar duniya kan zaɓen 2027, la’akari da girma ayyukan EU da suka gabatar.














