ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunansu (5)

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Zazzau

Bayanin baka ya nuna cewar Tera na daya daga cikin masu neman sarautar Ngazargamu a tsohuwar daular Borno kuma su suke sarautar a jamhuriyar Nijar wanda har yanzu suna da kyakkyawar alaka da junansu.

Wasu daga cikin jama’ar Kanuri da suke zaune a Geidam wanda a halin yanzu take cikin jihar Yobe sun guje wa jihadin Rabeh a cikin shekara ta 1890, wanda ya kai su ga gangarowa ya zuwa Gwara wadda aka fi sani da Gora.Wannan gari na kusa da garin Shani a cikin kasar Borno.

  • Wata Kungiya Ta Shirya Samar Da Gidaje Masu Saukin Kudi 400,000 A Nijeriya
  • Jihar Benuwai Ta Bankado Mutum 35 Masu Yi Wa Sirin Tattara Harajinta Zagon-Kasa

Auratayya da kabilar Kanakuru kuma a dalilin haka suka samar da kabilar Komberi, ita ma wannan kabilar ta jirga ya zuwa gundumar Tera.Yake-yaken jihadi sun ci gaba kuma jama’a sun ci gaba da hijira daga wannan wuri zuwa wancan wuri har ya zuwa shekara ta 1808 inda Fulani suka kama yammacin Ngazargamu wanda yake shi ne birnin daular Borno. Amma daga karshe a cikin shekara ta 1809 Sheikh Lamido ya kori Fulani daga daular Borno.

ADVERTISEMENT

Wannan kai-komo ya sa Rabe ya rasa wajen zama inda ya bar Zindar ya tafi ya zuwa gabashin Nijar a cikin shekara ta 1893. Wannan ya zo daidai da Turawan Faransa sun shigo kasar Nijar kuma suka kashe shi a wani gari mai suna Kousseri cikin kasar Kamaru a shekara ta 1900.Hakan lamarin ya faru ga dansa da shi wanda aka kashe shi a wani gari mai suna Gujba ta hanyar yaudara wanda Turawan Faransa su kai masa a shekara ta 1901.A can ne kuma Turawan Faransa suka hadu da Turawan Ingila kuma turawan Ingila suka nuna wa Turawan Faransa cewar sun wuce iyaka kasar Faransa, wanda a yanzu suna cikin kasar da ake kira Nijeriya.Hakan ta faru a inda Faransawa suka ba Turawan Ingila wuri.

Masallacin fada

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

Sarki Makau

Dangane da rayuwar kasar Zazzau kuwa, Sarkin Zazzau Muhammadu Makau ya samar wa ‘yan-uwansa wurin zama ba tare da sun tsoma kansu cikin rikicin mulki da wasu suka haramta masu don bukatar mulkar kasarsu ba.Zazzagawan asali,sun mai da martani ga sabuwar masarautar Zazzau a inda suka tare mashigin dake tsakanin kudancin kasar zuwa kasar Zazzau domin tauye kasuwancin da ke tsakaninsu da jama’an kudancin kasar nan.Hakan nan ma sun taimaka wa Turawa wajen cin kasar Zazzau,domin daidai da wannan lokaci ne Turawa suka bullo.Zazzagawa sun taka babbar rawa wajen cin kasar Zazzau a wancan lokacin. A cikin rubuce rucen Hausa Fulani sun so karin yin bayanan ga jama’ar Zazzau ta dauri musamman a kan yadda ta kasance da Sarkin Zazzau Muhammadu Makau ta wajen neman kau da gaskiyar al’amurra. Kuma sun hada gabas da yamma wuri guda.Watau wajen dauko tarihi Barebari suka gauraya a cikin tarihin Zazzau ta dauri.Inda suka dauko tarihin Albarka wanda yake shi dan Sarkin Kukawa ne can cikin kasar Borno kuma ya zo kasar Zazzau a sanadiyyar rikicin Sarauta.Albarka bai da niyar zama kasar Zazzau sai dai ya yada zango ya wuce.Wannan ya faru ne a zamanin Sarkin Zazzau Alu Dan Sidi. Amma ga al’amarin Sarki sai ya jawo hankalinsa da ya zauna a nan kasar Zazzau.Sarki ya yi masa alkawarin bashi duk bakin inda ya yi jifa ta tsaya kyauta.Hakan kuma ta faru,wannan wuri ya kama tun daga bakin kotu ya yi iyaka da kwarin fadama.A dalilin haka ne wannan wuri ya samu sunansa (Albarkawa).Malam Usman Katuka Sabulu da ne ga Sarkin Kano Al-wali kuma jika ne a gidan Sarautar Zazzagawan dauri (Zazzau),inda Sarki Isyaku Jatau ya dauki ‘yar kaninsa Malam Muhammadu Megamo ya ba da aurenta ga Sarkin Kano Al-wali.Usman Katuka Sabulu ya zo kasar Zazzau wajen kakanninsa don koyon karatu da samun ilmin addinin Muslinci, kuma Allah ya nufa wajen arzikinsa ke nan a dalilin goyan bayan da ya ba juyin mulkin Filato Barno da kuma Hausa Fulanin a kasar Zazzau,(domin suna kiran kansu a matsayin Fulani)a lokacin yi ma gidan kakanninsa bore don kaucewa halin da zai iya shiga bayan basu ko kuma a bisa wasu dalilai nasa.Daga karshe Sarkin Zazzau na farko a daular Hausa-Fulani a kasar Zazzau Malam Musa ya amince da Usman Sabulu kuma ya umurce shi da ya zauna a daya daga cikin gidajen kakanninsa watau na Zage zagi kuma aka ba shi sarautar katukan farko a daular Hausa Fulani.Katuka Usman ya samu tsawon Sarakuna biyu a daular Hausa Fulani kafin a tsige shi daga kan sarautar; wato Mu’sa dan Yamusa.

Zazzau
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

MASU ALAKA

Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Tarihi

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

May 30, 2026
Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya
Tarihi

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

February 22, 2026
Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959
Tarihi

Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959. (2)

January 11, 2026
Next Post
Shawarar Tabbatar Da Tsaron Duniya: Sin Ta Zo Da Mafita Ga Alkaba’in Tashe-tashen Hankula

Shawarar Tabbatar Da Tsaron Duniya: Sin Ta Zo Da Mafita Ga Alkaba’in Tashe-tashen Hankula

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.