ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunansu (5)

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Zazzau

Bayanin baka ya nuna cewar Tera na daya daga cikin masu neman sarautar Ngazargamu a tsohuwar daular Borno kuma su suke sarautar a jamhuriyar Nijar wanda har yanzu suna da kyakkyawar alaka da junansu.

Wasu daga cikin jama’ar Kanuri da suke zaune a Geidam wanda a halin yanzu take cikin jihar Yobe sun guje wa jihadin Rabeh a cikin shekara ta 1890, wanda ya kai su ga gangarowa ya zuwa Gwara wadda aka fi sani da Gora.Wannan gari na kusa da garin Shani a cikin kasar Borno.

  • Wata Kungiya Ta Shirya Samar Da Gidaje Masu Saukin Kudi 400,000 A Nijeriya
  • Jihar Benuwai Ta Bankado Mutum 35 Masu Yi Wa Sirin Tattara Harajinta Zagon-Kasa

Auratayya da kabilar Kanakuru kuma a dalilin haka suka samar da kabilar Komberi, ita ma wannan kabilar ta jirga ya zuwa gundumar Tera.Yake-yaken jihadi sun ci gaba kuma jama’a sun ci gaba da hijira daga wannan wuri zuwa wancan wuri har ya zuwa shekara ta 1808 inda Fulani suka kama yammacin Ngazargamu wanda yake shi ne birnin daular Borno. Amma daga karshe a cikin shekara ta 1809 Sheikh Lamido ya kori Fulani daga daular Borno.

ADVERTISEMENT

Wannan kai-komo ya sa Rabe ya rasa wajen zama inda ya bar Zindar ya tafi ya zuwa gabashin Nijar a cikin shekara ta 1893. Wannan ya zo daidai da Turawan Faransa sun shigo kasar Nijar kuma suka kashe shi a wani gari mai suna Kousseri cikin kasar Kamaru a shekara ta 1900.Hakan lamarin ya faru ga dansa da shi wanda aka kashe shi a wani gari mai suna Gujba ta hanyar yaudara wanda Turawan Faransa su kai masa a shekara ta 1901.A can ne kuma Turawan Faransa suka hadu da Turawan Ingila kuma turawan Ingila suka nuna wa Turawan Faransa cewar sun wuce iyaka kasar Faransa, wanda a yanzu suna cikin kasar da ake kira Nijeriya.Hakan ta faru a inda Faransawa suka ba Turawan Ingila wuri.

Masallacin fada

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

Sarki Makau

Dangane da rayuwar kasar Zazzau kuwa, Sarkin Zazzau Muhammadu Makau ya samar wa ‘yan-uwansa wurin zama ba tare da sun tsoma kansu cikin rikicin mulki da wasu suka haramta masu don bukatar mulkar kasarsu ba.Zazzagawan asali,sun mai da martani ga sabuwar masarautar Zazzau a inda suka tare mashigin dake tsakanin kudancin kasar zuwa kasar Zazzau domin tauye kasuwancin da ke tsakaninsu da jama’an kudancin kasar nan.Hakan nan ma sun taimaka wa Turawa wajen cin kasar Zazzau,domin daidai da wannan lokaci ne Turawa suka bullo.Zazzagawa sun taka babbar rawa wajen cin kasar Zazzau a wancan lokacin. A cikin rubuce rucen Hausa Fulani sun so karin yin bayanan ga jama’ar Zazzau ta dauri musamman a kan yadda ta kasance da Sarkin Zazzau Muhammadu Makau ta wajen neman kau da gaskiyar al’amurra. Kuma sun hada gabas da yamma wuri guda.Watau wajen dauko tarihi Barebari suka gauraya a cikin tarihin Zazzau ta dauri.Inda suka dauko tarihin Albarka wanda yake shi dan Sarkin Kukawa ne can cikin kasar Borno kuma ya zo kasar Zazzau a sanadiyyar rikicin Sarauta.Albarka bai da niyar zama kasar Zazzau sai dai ya yada zango ya wuce.Wannan ya faru ne a zamanin Sarkin Zazzau Alu Dan Sidi. Amma ga al’amarin Sarki sai ya jawo hankalinsa da ya zauna a nan kasar Zazzau.Sarki ya yi masa alkawarin bashi duk bakin inda ya yi jifa ta tsaya kyauta.Hakan kuma ta faru,wannan wuri ya kama tun daga bakin kotu ya yi iyaka da kwarin fadama.A dalilin haka ne wannan wuri ya samu sunansa (Albarkawa).Malam Usman Katuka Sabulu da ne ga Sarkin Kano Al-wali kuma jika ne a gidan Sarautar Zazzagawan dauri (Zazzau),inda Sarki Isyaku Jatau ya dauki ‘yar kaninsa Malam Muhammadu Megamo ya ba da aurenta ga Sarkin Kano Al-wali.Usman Katuka Sabulu ya zo kasar Zazzau wajen kakanninsa don koyon karatu da samun ilmin addinin Muslinci, kuma Allah ya nufa wajen arzikinsa ke nan a dalilin goyan bayan da ya ba juyin mulkin Filato Barno da kuma Hausa Fulanin a kasar Zazzau,(domin suna kiran kansu a matsayin Fulani)a lokacin yi ma gidan kakanninsa bore don kaucewa halin da zai iya shiga bayan basu ko kuma a bisa wasu dalilai nasa.Daga karshe Sarkin Zazzau na farko a daular Hausa-Fulani a kasar Zazzau Malam Musa ya amince da Usman Sabulu kuma ya umurce shi da ya zauna a daya daga cikin gidajen kakanninsa watau na Zage zagi kuma aka ba shi sarautar katukan farko a daular Hausa Fulani.Katuka Usman ya samu tsawon Sarakuna biyu a daular Hausa Fulani kafin a tsige shi daga kan sarautar; wato Mu’sa dan Yamusa.

Zazzau
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

MASU ALAKA

Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Tarihi

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

May 30, 2026
Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya
Tarihi

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

February 22, 2026
Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959
Tarihi

Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959. (2)

January 11, 2026
Next Post
Shawarar Tabbatar Da Tsaron Duniya: Sin Ta Zo Da Mafita Ga Alkaba’in Tashe-tashen Hankula

Shawarar Tabbatar Da Tsaron Duniya: Sin Ta Zo Da Mafita Ga Alkaba’in Tashe-tashen Hankula

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.