Majalisar Wakilai ta umurci kamfanonin rarraba wutar lantarki guda 11 (DISCOs) da su mayar da kuɗin da suka karɓa Naira biliyan ₦55.42 a ƙarƙashin shirin National Mass Metering Programme (NMMP).
Ƴan majalisar sun amince da rahoton kwamitinsu a ranar Alhamis, inda suka bai wa kamfanonin wa’adin watanni bakwai su biya bashin ga Central Bank of Nigeria (CBN). Shugaban kwamitin, Uchenna Okonkwo, ya ce binciken ya nuna cewa shirin bai cimma manufofin da aka sa gaba ba.
Ya bayyana cewa an ƙirƙiro shirin a 2020 domin rage giɓin mita, da inganta samar da mita a cikin gida, da daƙile asarar kuɗaɗen wuta da kuma kawo ƙarshen tsarin cajin kuɗi bisa hasashe. Daga cikin kamfanonin da suka amfana akwai na Abuja, da Eko, da Enugu, da Ibadan, da Ikeja, da Jos, da Kano da Yola, da sauransu.
Rahoton ya nuna cewa an ware jimillar ₦59.28bn ga kamfanonin, tare da sharaɗin mayar da kuɗin da riba kashi 9 cikin 100 kashi 6 ga masu zuba jari da kuma kashi 3 ga CBN. Sai dai binciken ya nuna cewa an fitar da ₦55.42bn kacal, yayin da aka kasa gano inda ₦3.85bn suka shiga.
Kwamitin ya kuma nuna damuwa kan wata yarjejeniya da ta bai wa kamfanin Meristem Wealth Management damar karɓar kashi 0.5 cikin 100 na kuɗaɗen shigar DISCOs duk shekara har zuwa 2030, inda aka ce tuni ya karɓi ₦450m.
Majalisar ta buƙaci ƙarin bayani kan tsarin kamfanin da ayyukan da ya gudanar, tare da amincewa da kafa kwamitin dawo da bashin haɗin gwuiwa tsakanin CBN da Hukumar lura samar da wutar lantarki ta ƙasa (NERC) kafin shekarar 2026.















Discussion about this post