ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tattaunawa Game Da Wankan Jego (2)

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Jego

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Lokaci ne na kula da jariri ba don wanka jego ba, da yanzu watakila mutum ko ganuwa ba zai yi ba ballantana ya dauki kansa a hoto. Domin kuwa kaina ya mole a lokacin da ake ciro ni daga cikin mahaifiyata. Amma cikin ikon Allah, kaka ta Ita ta rika gyara kan nan, tana gasa shi har sai da ya koma inda yake. Haka nan ana haifar yaro ya zo da matsalar cibi. Wato cibiya ta ki faduwa, su manya sun san yadda ake yi don ta fadi da sauri, idan ba ka bari an yi wa yaro ba zai cutu.

Lokaci ne na gyara, lokacin haihuwa gaban mace yana karuwa, wani lokacin ma sai an yanka wajen don yaro ya samu kofar fita wadatacciya. Su manyan mu sun san duk wata dabara da ake yi don gyaran wajen da kuma mayar masa da armashinsa don jin dadin maigida. Idan ba a yi haka ba, to kai ma ba za ka ji dadin saduwa ba.

  • Abubuwan Da Za Su Taimaka Wa Mai Azumi Ya Kasance Cikin Koshin Lafiya
  • Kula Da Fata Mai Maiko Da Ke Bata Kwalliya

 Lokaci ne na inganta lafiya a wannan lokacin ne ake ba wa uwargida duk wani nau’in abinci irin su sabaya, kunu, da sauran su don kara mata lafiya, da kara lafiyar mama don yaro ya samu ya sha. Ina da sani akan wannan, za ku ga wadanda suka haihu ba a Nijeriya ba suna samun matsaloli da dama kamar rashin ruwan mama wanda yaro zai sha kuma yana da kyau yaro kar ya fara da komai sai da ruwan nonon babarsa saboda yana da amfani sosai a jikinsa.

Lokaci ne na hutu, bayan haihuwa mace tana bukatar hutu. Hutu daga kicin, daga hidimar gida, da sauransu. Idan ba ta samu hutun da ya dace ba, to za ta iya lalacewa, jikinta ya sakwarkwace kamar tsohuwar mota musamman ma idan haihuwa ta zo da CS. Dole ta huta, dole a kula da ita.

Illolin tafiya gida wanka Jego

Yana bude kofofin matsala bincike da bayanai na masana matsalolin aure ya tabbatar da cewa da yawa daga cikin maza wanda su kan tsinci kansu a cikin matsalar neman mata banza ya samo asali ne a lokacin da matan su suka tafi gida wankan jego.

Wani namijin ko da baya harkar banza, ganin ya samu sarari, ya kan dauki sabbin dabi’o’i irin su neman mata, shaye-shaye da sauran su.

Rashin samun mai kulawa da shi, kamar abin da ya shafi abincinsa, da sauran hidimomi, ya kan sa ya nema ta hanyar da bai dace ba.

Wani ma daga nan yake koyon dabi’ar zuwa hira majalisa ko zuwa gidajen kallo da sauran su.

Haka nan zuwa jego gida, yana haifar da zargi, domin kuwa, ita uwangida da zarar ta ga canji, za ta fara kawo abubuwa akanta, daga karshe sai ta rika zargin ya shiga cikin zamantakewar.

Bugu da kari, yana haifar da rashin lafiya, mata da yawa sun kamu da ciwon sanyi da ciwon hawan jini a sakamakon wanka jego. Yanayin wanka yana sanya jini ya hau. Don haka ma likitoci da dama suke hanawa. Amma idan da za a yi da kyau, to za a iya toshe wannan matsala.

za mu ci gaba mako zuwa idan Allah ya kai mu

Jego
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Tarihin Hadejia Da Sarakunanta (6)

Tarihin Hadejia Da Sarakunanta (6)

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.