Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yaba wa jami’an tsaro saboda kokarinsu na ceto dalibai 100 na wata makarantar Katolika da aka kai wa hari a Jihar Neja.
Yayin da yake bayyana farin cikinsa kan dawowar daliban, Shugaba Tinubu ya umarci jami’an tsaro da su tabbatar da gaggauta kuButar da sauran dalibai 115 da malamansu da har yanzu suke tsare a hannun masu garkuwa da su.
Wannan bayani ya fito ne daga Bayo Onanuga, Mashawarci na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai da Tsare-tsare, a wata sanarwa da ya fitar a Abuja, ranar Litinin.
- Ƙirƙirar Hisbah Mai Zaman Kanta: Kungiyar Lauyoyi ‘Yan Kano Ta Shigar Da Tinubu Ƙara
- Tinubu Na Ɗaukar Ƙwararan Matakai Don Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya – Shettima
Onanuga ya ce Shugaba Tinubu ya tabbatar wa iyayen daliban cewa gwamnatin tarayya da ta Jihar Neja suna aiki tare don ganin an hada dukkan daliban da aka sace da iyalansu cikin koshin lafiya.
A wani bangare na sanarwar an ce, “An sanar da ni game da dawowar dalibai 100 na makarantar Katolika da ke Jihar Neja cikin koshin lafiya. Ina murna tare da Gwamna Umar Bago kuma ina yaba wa jami’an tsaro bisa jajircewarsu wajen tabbatar da komawar daliban wurin iyalansu tun bayan mummunan lamarin da ya faru a ranar 21 ga Nuwamba.
“Umarna ga jami’an tsaro har yanzu ita ce cewa dole ne a ceto dukkan daliban da sauran ‘yan Nijeriya da aka yi garkuwa da su a fadin kasar nan, a dawo da su gida cikin aminci. Dole ne mu tabbatar da an kirga duk wanda lamarin ya rutsa da shi.
“Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da aiki tare da Jihar Neja da sauran jihohi don tsare makarantu da kuma samar da ingantacciyar muhalli mai aminci da dacewa domin karatun ‘ya’yanmu.
“Daga yanzu, jami’an tsaro tare da gwamnonin jihohi dole su hana afkuwar garkuwa da mutane a nan gaba. Ya kamata yaranmu su daina zama abin hari ga mugayen ‘yan ta’adda da ke kokarin dakile iliminsu tare da jefa su da iyayensu cikin azaba marar misaltuwa.”














