Rundunar ‘Yansandan Jihar Kwara ta kama mutane uku da ake zargi da ɓarnata kayayyakin gwamnati da kuma fashi da makami a birnin Ilorin.
An kama waɗanda ake zargin ne a ranar Talata a yankin Asa Dam/Dangote da ke Ilorin ta hannun jami’an sabon sashen yaƙi da manyan laifuka.
Kakakin rundunar, Adetoun Ejire-Adeyemi, ta ce an kama su ne bayan samun bayanan sirri da kuma ƙorafe-ƙorafen jama’a kan ayyukan ‘yan bindiga a yankin.
Ta ce bincike ya nuna cewa waɗanda ake zargin na cikin wata ƙungiya da ke sata da lalata fitilun titi da gwamnati ta saka, tare da yin fashi a wasu sassan Ilorin.
An gano kayayyaki a hannunsu da suka haɗa da bindigogi guda biyu da aka ƙera a gida, kayan aiki, da kuma wasu ƙwayoyi da ake zargin miyagun ƙwayoyi ne.
‘Yansanda sun ce suna ci gaba da bincike domin gano sauran mambobin ƙungiyar da kuma waɗanda ke karɓar kayayyakin sata.















Discussion about this post