Tsohon Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi gargaɗin cewa Amurka na iya sake ƙaddamar da hare-hare a Nijeriya idan, a cewarsa, aka ci gaba da kashe Kiristoci a ƙasar. Trump ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da jaridar New York Times wadda aka wallafa a ranar Alhamis.
A cewar Trump, ya taba yin tunanin kai hari sau ɗaya, amma ya ce idan abin aka ci gaba da kisan Kiristoci to Amurka ba za ta yi ƙasa a gwuiwa ba wajen sake ɗaukar matakin soji a Nijeriya. Wannan kalamai nasa sun sake tayar da ƙura a matakin ƙasa da ƙasa, musamman dangane da batun tsaro da rikice-rikicen da ke addabar Nijeriya.
- Trump Zaman Lafiya Yake Samar Wa Nijeriya Ba Yaƙi Ba – Riley Moore
- Trump Ya Caccaki Kasashen Turai Bayan Ayyana Nahiyar A Matsayin Mai Rauni
Sai dai gwamnatin Najeriya ta sha musanta zargin cewa kashe-kashen da ke faruwa a sassan ƙasar na da alaƙa da addini kawai. Jami’an gwamnati sun jaddada cewa matsalolin tsaron ƙasar sun shafi ta’addanci, da fashi da makami, da rikicin makiyaya da manoma, da sauran laifuka, ba wai kai tsaye kisan Kiristoci ba.
Masu lura da al’amuran siyasa da tsaro na ganin kalaman Trump na iya ƙara dagula fahimtar matsalar tsaron Nijeriya a idon duniya, tare da jawo matsin lamba daga ƙasashen waje. Har yanzu dai babu wata sanarwa a hukumance daga gwamnatin Amurka kan yiwuwar ɗaukar irin wannan mataki a kan Nijeriya kamar yadda BBC Hausa ta rawaito.















Discussion about this post