ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wakilin Sin Ya Bukaci A Kai Zuciya Nesa Domin Kaucewa Kara Tabarbarewar Yanayi A Gabas Ta Tsakiya

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Sin

Wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Fu Cong, ya yi kira ga dukkanin sassa masu ruwa da tsaki da su kai zuciya nesa, su kaucewa furta kalamai da ka iya ta’azzara lamura, kana su kauracewa aiwatar da matakan ta da husuma, domin kaucewa kara tabarbarewar yanayin zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya.

 

Fu Cong, wanda ya yi kiran a jiya Litinin, yayin zaman MDD da aka gudanar game da batun aiwatar da sakamakon manyan tarukan MDD, da batun karfafawa, da aiwatar da sauye-sauye ga tsarin ayyukan majalisar, ya kuma koka game da yadda batun Falasdinu ya zamowa duniya “kadangaren bakin tulu”. Fu ya kuma yi kashedin cewa, a kullum tashin hankali a Gaza na ci gaba da tsawaita, tare da hallaka karin fararen hula, yayin da kuma a baya-bayan nan ya bazu zuwa kasar Lebanon, a gabar da cikakken yaki ke neman barkewa a Gabas ta Tsakiya baki daya.

ADVERTISEMENT
  • Imanin Sin Kan Ci Gaban Tattalin Arzikinta Zai Haifar Da Tasiri Mai Kyau
  • Kare Hakki Da Rayukan Mutane Ba Batu Ne Na Siyasantarwa Ko Nuna Fuska Biyu Ba

Jami’in ya ce, “Muna kira da a martaba ikon mulkin kai, da tsaro, da ikon kare hurumin daukacin yankunan dukkanin kasashe, kana muna adawa da dukkanin wasu matakai da ka iya keta ka’idojin cudanyar sassan kasa da kasa, tare da sukar dukkanin wasu hare-hare kan fararen hula.”

 

LABARAI MASU NASABA

Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

Game da batun kasar Ukraine kuwa, jakadan na Sin ya ce, har yanzu abu ne mai wahalar gaske a yi hasashen kawo karshensa, don haka akwai bukatar dukkanin sassa masu ruwa da tsaki da su sanya batun wanzar da zaman lafiya da moriyar al’umma gaban komai, kana su rungumi tattaunawar dawo da zaman lafiya, da shawo kan dukkanin rikici ta hanyar siyasa. (Saminu Alhassan)

 

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka
  • Sulaiman
    Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

MASU ALAKA

Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

July 27, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

July 27, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

July 27, 2026
Next Post
Ambaliyar Ruwa Ta Katse Hanyar Maiduguri Zuwa Damboa

Boko Haram Sun Sake Kai Wani Hari Kan Al'ummar Kirawa A Jihar Borno

LABARAI MASU NASABA

Sin

Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro

July 27, 2026
Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

July 27, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

July 27, 2026
Sin

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

July 27, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

July 27, 2026
Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026
Sin

WAFU B 2026: Nijeriya Ta Doke Ghana Da Ci 4-2 A Wasan Farko

July 27, 2026
An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

July 27, 2026
Sin

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

July 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.