Memban hukumar siyasa ta kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta Sin, kana ministan harkokin wajen kasar Wang Yi ya tattauna da babban sakataren kungiyar hadin kan musulmai (OIC) Hussein Ibrahim Taha, a yau Litinin 26 ga watan nan a birnin Beijing.
Wang Yi ya bayyana cewa, bangaren Sin a ko da yaushe yana mayar da hankali matuka kan inganta dangantakarta da kasashen musulmi, da kungiyar OIC bisa manyan tsare-tsare. Ya kuma yaba da goyon bayan da kasashen musulmi suke nunawa bangaren Sin, a kan batutuwan da suka shafi yankin Xinjiang da Taiwan. Ya kuma ce, bangaren Sin yana fatan kara hadin kai da kasashen musulmai wajen kare hakkin da ya dace na kasashe masu tasowa, tare da adawa da dawowar ra’ayin “dokar daji”, wato fin karfi da babakere.
A nasa bangaren, Taha ya bayyana cewa, kungiyar OIC tana rike da ka’idar kasar Sin daya tak a duniya, tana yabawa babban nasarar da yankin Xinjiang ta samu, kuma tana adawa da tsoma baki cikin al’amuran cikin gida na Sin da wasu kasashe ke yi.
Ya ce, kungiyar tana son yin hadin gwiwa da bangaren Sin, a fannin karfafawa, da zurfafa dangantakar abokantaka cikin kwarin gwiwa, kuma tana yabon gagarumar gudunmawar da bangaren Sin ya bayar, wajen magance batun Palasdinu daga dukkan fannoni mai dorewa cikin adalci. (Amina Xu)















Discussion about this post