• English
  • Business News
Monday, June 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wani Mutum Ya Yanke Marainansa Yana Barci, Ya Dauka Nama Ne A Ghana

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Al'ajabi
0
Wani Mutum Ya Yanke Marainansa Yana Barci, Ya Dauka Nama Ne A Ghana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani manomi a kasar Ghana mai suna Kofi Atta a halin yanzu na kwance a asibiti cikin wani mawuyacin hali bayan da ya yanke marainansa a lokacin da yake tsaka da barci.

Atta, ya shaida wa BBC a kan gadon jinya ya yi bayanin yadda lamarin ya faru daki-daki, inda likitoci ke ta kokarin duba yadda za su yi masa aiki.

  • Dangantakar Sin Da Kasashen Afirka: Yabon Gwani Ya Zama Dole
  • Sanata Uba Sani Ya Karyata Rahoton Kudurin Kirkiro Sabuwar Jihar Zazzau

Ya ce a yanzu dai ana sa masa karin ruwa ne tare da wasu allurai da ake ta yi masa, amma dai sai an yi masa tiyata.

Ya kara da cewa a yanzu ba shi da ko kudin da zai biya motar asibitin da za ta dauke shi zuwa babban asibitin koyarwa na Komfo Anokye, da ke Kumasi a kasar ta Ghana, inda a can ne za a iya yi masa babbar tiyata.

Mutumin ya ce, yana barci ne na kailula ne a kan wata kujera sai ya yi mafarki cewa yana yanka nama da ke ajiye a gabansa, wanda zai dafa abinci da shi, inda a cikin barcin ya janyo wuka ya yanke marainan nasa.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

Atta, ya ce abin ya ba shi mamaki kwarai domin har lokacin da wasu makwabtansa biyu suka kawo masa agaji bai san me ya faru ba, sai da ya tashi daga kan kujerar ya rika jin wani zafi a gabansa ga kuma jini na zuba.

Mutumin ya ce, har lokacin da aka kawo masa daukin ba shi tabbacin kan abin da ya faru, ji yake kamar yana mafarki ne.

Ya ce shi kansa bai san yadda aka yi ya dauko wukar ba, ”abin ya daure min kai,” in ji shi.

Manomin mai shekara 47 wanda ke garin Assim Akomfode a kasar, har bayan da ya yanke marainan nasa yana cikin barci har ya yi kururuwar neman taimako bai farka ba yana cikin mafarki ne domin shi duk bai san abin da ya faru ba a lokacin.

Ya ce duk da cewa makwabtansa sun kawo masa dauki inda ya rika jin zafi a gabansa ga kuma jini yana zuba, bai fahimci abin da ya faru ba, sai daga baya a gadon asibiti hankalinsa ya dawo ya san abin da ya faru.

A fagen ilimin kula da lafiya, akwai wata larura wadda ake kira ‘Parasomnia’ a Turance, inda mutum kan aikata wasu abubuwa sabanin na hankali a lokacin da yake barci.

Wannan larura takan sa mutum ya rika tafiya ko maganganu ko fitsarin kwance ko mugun mafarki ko kikkifta ido da dai sauran abubuwa na daban a lokacin da yake barcin.

A lokacin da mutum yake cikin wannan hali wasu da ke tare da shi ko kusa da shi za su ga kamar ba barci yake ba yana farke ne, to amma yana cikin yanayi ne na barci bai san abin da yake yi ba.

Mutanen da ke cikin wannan yanayi ba ma sa iya tuna abin da ya faru da su ko abin da suka aikata a lokacin da suke cikin halin.

Bayanai sun nuna cewa abin da mutum kan yi a wannan lokacin kamar yana aikata abin da mafarkinsa ya kunsa ne a zahiri.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BarciGhanaLaruraMafarkiManomiMaraina
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dangantakar Sin Da Kasashen Afirka: Yabon Gwani Ya Zama Dole

Next Post

Amurka Za Ta Sake Dandana Kudar Da Ta Taba Dandanawa A Kabul

Related

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi
Al'ajabi

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

3 weeks ago
An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano
Al'ajabi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

1 month ago
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa

1 month ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi

2 months ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Mahaifiyarsa Da Taɓarya A Bauchi

3 months ago
‘Yansanda Sun Dakile Harin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Kan Wasu Rukunin Gidaje A Katsina
Al'ajabi

Wani Jami’in Ɗansanda Ya Bindige Kansa Har Lahira A Jihar Nasarawa

4 months ago
Next Post
Amurka Za Ta Sake Dandana Kudar Da Ta Taba Dandanawa A Kabul

Amurka Za Ta Sake Dandana Kudar Da Ta Taba Dandanawa A Kabul

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas

Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas

June 16, 2025
Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya

Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya

June 15, 2025
Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC

Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC

June 15, 2025
PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin

PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin

June 15, 2025
An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 27 Na Shanghai

An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 27 Na Shanghai

June 15, 2025
Yansanda Sun Fara Tsananta Daukar Mataki Kan Yan Daba A Kano

Yansanda Sun Fara Tsananta Daukar Mataki Kan Yan Daba A Kano

June 15, 2025
Dan Asalin Tudun Loess

Dan Asalin Tudun Loess

June 15, 2025
Ba Zai Manta Da Shawarar Mahaifinsa Ba

Ba Zai Manta Da Shawarar Mahaifinsa Ba

June 15, 2025
Ganduje Ya Noƙe Kan Furta Ko Shettima Zai Yi Takara Da Tinubu A 2027

Ganduje Ya Noƙe Kan Furta Ko Shettima Zai Yi Takara Da Tinubu A 2027

June 15, 2025
Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila

Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila

June 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.