ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wani Yaro Dan Shekara 12 Ya Harbe Mahaifiyarsa ‘Yar Nijeriya A Amurka

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Amurka

Wani yaro karami dan shekara 12 ya harbe tare da hallaka mahaifiyarsa ‘yar Nijeriya mai suna Ayobiyi Cook, kodayake da farko yaron ya so boye gaskiyar abun da ya faru, a cewar hukumomin a kasar Amurka.

Ofishin Jefferson County Sheriff da ke Alabama ya ce a ranar Litinin jami’ansa sun fara gudanar da bincike kan musabbabin mutuwar wata mace mai shekara 29 a Forestdale da ke Alabama.

  • Dole Ne A Hukunta Kasar Amurka Wadda Ta Fi Keta Hakkin Dan Adam A Duniya

A lokacin binciken, masu binciken sun gano cewa dan Cook mai shekara 12 a duniya (ba a bayyana sunansa ba) ya ciro bindiga ba da gangan ba inda ya bude wa Mamarsa wuta tare da kasheta.

ADVERTISEMENT

“Yaron ya kirkiri labari da masu bincike suke ganin hakan ba zai faru ba,” a cewar sanarwar ofishin Sheriff.

“Amma daga baya yaron ya yi bayanin hakikanin abun da ya faru.”

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Masu bincike sun ce hujjoji ya nuna cewa harbin da yaron ya yi ba bisa gangan ya yi ba.

Yaron wanda ya tare da iyalansa har yanzu an ce kotun kula da tsarin iyali ne zai kula da kes din.

Bayanan farko da sashin binciken ya fitar, ya ce babu wani alamar fita da karfi a gidan lokacin da suka je inda abun ya faru, sai dai wani ya gudu daga gidan bayan an kira lambar 911.

Mijin matar mai suna Djuan Cook, ya wallafa a shafinsa na Facebook cewa za a bisne matar a ranar 12 ga Agustan.

A 2022 zuwa yanzu, yara sun yi harbin ba na gangan ba har guda 169 kamar yadda wata cibiya mai fadakarwa kan illar amfani da bindiga ba bisa ka’ida ba wato Everytown for Gun Safety ta shaida.

Harbe-harben yaran ya janyo mutuwar 74 a jikkata 104 a Amurka a cikin wannan shekarar.

A shekarar 2021, harbin da ba na ganganci ba guda 392 ne aka samu rahoton faruwarsu a Amurka da ya janyo mutuwar 163 da jikkata wasu 248.

Amurka
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
Labarai

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Next Post
Kotu Ta Amince Da Bayar Da Belin Wanda Ya Yi Garkuwa Da Yayarsa A Zariya

Kotu Ta Amince Da Bayar Da Belin Wanda Ya Yi Garkuwa Da Yayarsa A Zariya

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026
Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.