ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasannin Cin Kofin Nahiyar Afirka Na Mata Sun Kankama

by Abba Ibrahim Wada
4 years ago
Afirka

A ranar biyu ga watan Yuli aka fara gasar kwallon kafar mata a gasar cin kofin nahiyar Afirka da kasar Morocco za ta karbi bakunci, wadda ake kira Women’s Africa Cup of Nations (WAFCON).

Nijeriya kasar da ta lashe gasar a baya, ta tafi da ‘yar wasa Asisat Oshoala da Ashleigh Plumptre cikin tawagarta da ta halarci gasar, sai dai kociyan tawagar Randy Waldrum, ya cire sunan ‘yan wasa Gift Monday da Ngozi Okobi-Okeoghene daga tawagarsa.

  • Mane Ya Zama Dan Wasa Na 10 A Buga Wa Bayern Munchen Wasa

Sai dai farko tun da hukumar kwallon kafar kasar ta NFF ta shiga tsaka mai wuya lokacin da take son rage sunayen yan kwallon daga 32 zuwa 28 da za a halarci gasar da su, kawo yanzu ‘yan wasan Nijeriya 28 da za su wakilci Nijeriyar a wannan babbar gasa, suna Moroko domin buga gasar kuma tuni su ka yi rashin nasara a wasan farko da ci 2-1 hannun ‘yan wasan kasar Afirka ta Kudu.

ADVERTISEMENT

An fara gasar Afirka ta mata ta WAFCON 2022 a ranar 2 ga watan Yuli zuwa 23 , kuma za a yi gasar a Moroko sannan tawagar Nijeriya da ake kira Super Falcons ta fafata da Bayana-Bayana ta Afrika ta Kudu a ranar 4 ga watan Yuli a matakin rukunin C sai sauran kasashe biyun da ke cikin wannan rukuni sun hada da Burundi da Botswana.

Kasashe 12 ne za su buga wannan gasa wadda za ta gudana a Morocco. Hukumar kwallon kafa ta Afirka, CAF ta rarraba kasashen zuwa rukuni uku dauke da kasashe hudu kowanne kamar yadda aka saba.

LABARAI MASU NASABA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

Rukunin A:

Morocco da Burkina Faso da Senegal da kuma Uganda.

Rukunin B:
Kamaru da Zambia da Tunisia da kuma Togo sai

Rukunin C: Nijeriya da Afirka ta Kudu da Burundi da kuma Botswana.

A shekarar 2021 ba a samu damar gudanar da wannan gasa ba saboda annobar Korona, kuma gasar da za ta gudana a Arewacin Africa, ita ce ta farko da aka buga daga kasashe 8 zuwa 12.

Kamar ko wacce irin gasa, akan samun kasashen da suke halartar a karon farko a wannan shekarar ma an samu wasu kasashen guda hudu da suka zo a karon farko da suka hada da Togo da Burundi da Burkina Faso da kuma Botswana.

Kasar da ke kan gaba cikin jerin kasashe ita ce Nijeriya, Super Falcons kuma na daya a kungiyoyin Afrika ta 39 a duniya kuma gasa uku ta baya da ta gudana Nijeriya ce ta lashe, kuma karo tara da ta lashe a jumulla.

‘Yar wasanta mai buga wasa a Barcelona Assisat Oshola ita ce ta fi kowacce buga wasa a gasar, sannan ita ce ta lashe takalmin zinare a babbar gasar kwallo ta mata ta Sifaniya kuma ta ci kwallo 20 cikin wasa 19 da ta buga, kuma an ba ta kyautar ne tare da ‘yar kasar Brazil Geyse Ferreira wadda ta ci kwallo 20 a wasanni 27 da ta yi.

Kasashe hudu da za su kai karawar dab da na karshe a gasar kofin Afirka ta bana, su ne za su wakilci Afirka a gasar kofin duniya ta mata da za a yi a shekarar 2023, sai sauran kungiyoyin biyu za su yi wasan samun gurbi ne da za a fafata tsakanin kasashen 10 domin halartar kofin duniya da za a yi a kasashen Australia da New Zealand.

AFIrka
Abba Ibrahim Wada
+ postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Har Yanzu Nijeriya Tana Fatan Zuwa Kofin Duniya Na 2026
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Mece Ce Matsalar Real Madrid? 
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Ko Ka San Dalilin Da Zai Bai Wa Nijeriya Damar Zuwa Gasar Cin Kofin Duniya?

MASU ALAKA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA
Wasanni

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa
Wasanni

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City
Wasanni

Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

July 5, 2026
Next Post
Uwa Ta Yi Shahada Bayan Karya Dan Bindiga Da Tabarya Wajen Kare Danta

Uwa Ta Yi Shahada Bayan Karya Dan Bindiga Da Tabarya Wajen Kare Danta

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Montenegro Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.