• Leadership Hausa
Friday, December 8, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasannin Cin Kofin Nahiyar Afirka Na Mata Sun Kankama

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
in Wasanni
0
Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar biyu ga watan Yuli aka fara gasar kwallon kafar mata a gasar cin kofin nahiyar Afirka da kasar Morocco za ta karbi bakunci, wadda ake kira Women’s Africa Cup of Nations (WAFCON).

Nijeriya kasar da ta lashe gasar a baya, ta tafi da ‘yar wasa Asisat Oshoala da Ashleigh Plumptre cikin tawagarta da ta halarci gasar, sai dai kociyan tawagar Randy Waldrum, ya cire sunan ‘yan wasa Gift Monday da Ngozi Okobi-Okeoghene daga tawagarsa.

  • Mane Ya Zama Dan Wasa Na 10 A Buga Wa Bayern Munchen Wasa

Sai dai farko tun da hukumar kwallon kafar kasar ta NFF ta shiga tsaka mai wuya lokacin da take son rage sunayen yan kwallon daga 32 zuwa 28 da za a halarci gasar da su, kawo yanzu ‘yan wasan Nijeriya 28 da za su wakilci Nijeriyar a wannan babbar gasa, suna Moroko domin buga gasar kuma tuni su ka yi rashin nasara a wasan farko da ci 2-1 hannun ‘yan wasan kasar Afirka ta Kudu.

An fara gasar Afirka ta mata ta WAFCON 2022 a ranar 2 ga watan Yuli zuwa 23 , kuma za a yi gasar a Moroko sannan tawagar Nijeriya da ake kira Super Falcons ta fafata da Bayana-Bayana ta Afrika ta Kudu a ranar 4 ga watan Yuli a matakin rukunin C sai sauran kasashe biyun da ke cikin wannan rukuni sun hada da Burundi da Botswana.

Kasashe 12 ne za su buga wannan gasa wadda za ta gudana a Morocco. Hukumar kwallon kafa ta Afirka, CAF ta rarraba kasashen zuwa rukuni uku dauke da kasashe hudu kowanne kamar yadda aka saba.

Labarai Masu Nasaba

Iwobi Ya Jefa Kwallo 2 Yayin Da Fulham Ta Lallasa Forest Da Ci 5-0

Bai Kamata Chelsea Ta Zauna A Matsayi Na 10 A Gasar Firimiya Ba – Pochettino

Rukunin A:

Morocco da Burkina Faso da Senegal da kuma Uganda.

Rukunin B:
Kamaru da Zambia da Tunisia da kuma Togo sai

Rukunin C: Nijeriya da Afirka ta Kudu da Burundi da kuma Botswana.

A shekarar 2021 ba a samu damar gudanar da wannan gasa ba saboda annobar Korona, kuma gasar da za ta gudana a Arewacin Africa, ita ce ta farko da aka buga daga kasashe 8 zuwa 12.

Kamar ko wacce irin gasa, akan samun kasashen da suke halartar a karon farko a wannan shekarar ma an samu wasu kasashen guda hudu da suka zo a karon farko da suka hada da Togo da Burundi da Burkina Faso da kuma Botswana.

Kasar da ke kan gaba cikin jerin kasashe ita ce Nijeriya, Super Falcons kuma na daya a kungiyoyin Afrika ta 39 a duniya kuma gasa uku ta baya da ta gudana Nijeriya ce ta lashe, kuma karo tara da ta lashe a jumulla.

‘Yar wasanta mai buga wasa a Barcelona Assisat Oshola ita ce ta fi kowacce buga wasa a gasar, sannan ita ce ta lashe takalmin zinare a babbar gasar kwallo ta mata ta Sifaniya kuma ta ci kwallo 20 cikin wasa 19 da ta buga, kuma an ba ta kyautar ne tare da ‘yar kasar Brazil Geyse Ferreira wadda ta ci kwallo 20 a wasanni 27 da ta yi.

Kasashe hudu da za su kai karawar dab da na karshe a gasar kofin Afirka ta bana, su ne za su wakilci Afirka a gasar kofin duniya ta mata da za a yi a shekarar 2023, sai sauran kungiyoyin biyu za su yi wasan samun gurbi ne da za a fafata tsakanin kasashen 10 domin halartar kofin duniya da za a yi a kasashen Australia da New Zealand.

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Haifi Wani Yaro Da Hannu Hudu Da Kafa Hudu A Indiya

Next Post

Uwa Ta Yi Shahada Bayan Karya Dan Bindiga Da Tabarya Wajen Kare Danta

Related

Iwobi Ya Jefa Kwallo 2 Yayin Da Fulham Ta Lallasa Forest Da Ci 5-0
Wasanni

Iwobi Ya Jefa Kwallo 2 Yayin Da Fulham Ta Lallasa Forest Da Ci 5-0

1 day ago
Bai Kamata Chelsea Ta Zauna A Matsayi Na 10 A Gasar Firimiya Ba – Pochettino
Wasanni

Bai Kamata Chelsea Ta Zauna A Matsayi Na 10 A Gasar Firimiya Ba – Pochettino

1 day ago
Manchester City Tayi Rashin Nasara A Hannun Aston Villa Da Ci 1-0
Wasanni

Manchester City Tayi Rashin Nasara A Hannun Aston Villa Da Ci 1-0

1 day ago
Dan Kwallon Kano Pillars Ya Zazzaga Kwallaye Biyar A Ragar Gombe United 
Wasanni

Dan Kwallon Kano Pillars Ya Zazzaga Kwallaye Biyar A Ragar Gombe United 

5 days ago
Manchester City Ta Koma Ta Uku A Teburin Firimiya Bayan Buga Canjaras Da Tottenham
Wasanni

Manchester City Ta Koma Ta Uku A Teburin Firimiya Bayan Buga Canjaras Da Tottenham

5 days ago
Donnarumma Ya Samu Katin Kora Bayan Minti 10 Da Fara Wasa.
Wasanni

Donnarumma Ya Samu Katin Kora Bayan Minti 10 Da Fara Wasa.

5 days ago
Next Post
Uwa Ta Yi Shahada Bayan Karya Dan Bindiga Da Tabarya Wajen Kare Danta

Uwa Ta Yi Shahada Bayan Karya Dan Bindiga Da Tabarya Wajen Kare Danta

LABARAI MASU NASABA

kwastam

Hukumar Kwastam A Kano Ta Samu Kudin Shiga Naira Biliyan 6.9 A Nuwamba

December 8, 2023
Al’ajabi: Saurayi Ya Yi Wa Zakara Fyade A Adamawa

Al’ajabi: Saurayi Ya Yi Wa Zakara Fyade A Adamawa

December 8, 2023
tallafi

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Raba Tallafi Ga Masu Kananan Masana’antu

December 8, 2023
Akpabio

‘Yan Nijeriya Ba Sa Amanna Da Jam’iyyun Siyasa – Akpabio

December 8, 2023
Manzon Allah

Daga Cikin Mutane Aka Aiko Manzon Allah Amma Ba Mutum Ne Kamar Kowa Ba (SAW)

December 8, 2023
Kyautata Rayuwar Matasa Ne Fatanmu – Kwamoti La’ori 

Kyautata Rayuwar Matasa Ne Fatanmu – Kwamoti La’ori 

December 8, 2023
Ba Za A Cimma Wannan Yarjejeniya Ba Tare Da Taimakon Sin Ba

Ba Za A Cimma Wannan Yarjejeniya Ba Tare Da Taimakon Sin Ba

December 8, 2023
NAHCON

Hajjin 2024: NAHCON Za Ta Sabunta Ka’idojin Ciyar Da Alhazai Da Masaukansu

December 8, 2023
kaduna

Matsalar Da Ta Haddasa Harin Bom Na Kaduna

December 8, 2023
Ministan Yaɗa Labarai Ya Kafa Kwamitin Tsara Cusa Ɗa’a Da Kishin Ƙasa

Ministan Yaɗa Labarai Ya Kafa Kwamitin Tsara Cusa Ɗa’a Da Kishin Ƙasa

December 7, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.