ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Halayen Da Maza Ke Nuna Wa Uwargida In Sun Shirya Karin Aure

by Amina Usman
3 years ago
Uwargida

Kamar yadda aka sani aure wani nau’i ne na ibada wanda yake haifar da nishadi natsuwa da jin dadi. Idan aka ce aure ana nufin sadaukarwa da kuma girmama juna.

Zamantakewar aure abu ne da aka gina shi a kan abubuwa biyu zuwa uku na farko akwai kishin juna na biyu akwai yarda da amana. Idan muka dauki yarda da amana zamu ga cewa wani abu ne da ma’auratan biyu suka damkawa junansu inda zamu ga cewa miji yana kokarin kare duk wani martaba na matarsa haka itama matar.

  • Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Matsayinta Na Warware Matsalar Ukraine A Siyasance
  • Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC

Idan muka yi dubi da shimfidan da na fara zamu ga cewa an gina zaman aure a kan turaban sadaukarwa da amana, idan kuwa haka ne to me yasa Miji ke juya wa uwargida baya a lokacin da yake kokarin karo aure?

ADVERTISEMENT

Yawanci maza in sun yi shirin karin aure gaskiya akwai halayya iri daban-daban da uwargida ke cin karo da su a wurin Maigida ,wanda zamu ga cewa gaba daya miji yakan manta irin zaman dadi da kuma zaman hakuri da ta yi da shi.

Hakazalika miji yana sauyawa ta halayya daban-daban ga uwargida inda har wani lokaci in ba a kai zuciya nesa ba saki ko sabani mai karfi na iya shiga tsakani. Yawanci maza in sun zo karin aure sukan sauya fuska da walwala wa uwargida wanda hakan an yi ittifakin cewa yawanci maza suna ganin cewa si yanzu ita uwargida ta ragwaba bata da sauran mamora shiyasa idon su sai ya kyalla ya fara hango musu wata a waje,wanda har zai kai ga ana diban lokacin uwargida ana baiwa amarya tun kafin ta shigo gidan.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Wani lokaci zakaga idan miji ya fara shirin karin aure zai dauko wasu sababbin halayya wanda uwargida bata sansu ba ya dorawa kansa, kamar misali akwai mijin da zakaga idan yaso karin aure to fa uwargida ta shiga uku don komai ta yi ba ta burge shi ba saima hantara da fada da zai dinga yawan yi mata, ko kuma kaga wani mijin in yaso karin aure to ya daina shiga harkan uwargida musamman da muke da kafafen soshiyal media daban-daban to gaba daya lokacin shi ya zama na amarya ko yaushe suna manne a waya ko kuma suna ‘Charting’ ita uwargida an ajiyeta a gefe an gama yayin ta.

Wani namijin in yaso aure kuma yarasa wani laifi zai mannawa uwargida in aka dameshi da tamabaya wani sai yace ai bata iya tarban baki ba ne saboda a tunanin sa yana ganin kamar ita wacce yake kokarin aurowar tafi kowa hankali ta iya komai dari bisa dari bai san cewa hangen dala yake yi ba. Wani namijin kuwa sababbin halayensa basa chanzawa sai ya auro ta ya kawo cikin gida daga nan ne labari zai chanza salo in ya hadu da itama amaryar ‘yar garice sai su hada kai da mijin su muzgunawa uwargida, misali akwai gidan da za kaga daga ranar da amarya ta zo to fa baban maganar wanda miji zai saurara akwai gidan da naga amarya ta yi wa uwargida sharrin cewa tana bin malamai saboda tana gane ganecin tana bacci irin wannan sharrin kamata ya yi ace mijin ya yi hukunci mai karfi amma abin mamaki sai ya goyi bayan amarya a kan cewa ya yarda uwargida na bin boka. Mai yasa, duk tsawon shekarun da suka yi da uwargidan bai fada mata tana bin malamai ba saida ya karo aure, abubuwa makamantan haka suna faruwa a gidajen aure daban daban a duk sanda miji ya dau kdamaran karo aure.

Uwargida
Amina Usman
+ postsBio
  • Amina Usman
    https://hausa.leadership.ng/author/amina-usman/
    Gasasshen Nama Mai Dankali
  • Amina Usman
    https://hausa.leadership.ng/author/amina-usman/
    Shawara Ga Ma’aurata Game Da Hassada
  • Amina Usman
    https://hausa.leadership.ng/author/amina-usman/
    Yadda Ake Miyar Zogale
  • Amina Usman
    https://hausa.leadership.ng/author/amina-usman/
    Amfanin Danyen Kwai Wajen Magance Kurajen Fuska

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Motsa Jiki Na Hana Kamuwa Da Muggan Cututtuka -WHO

Motsa Jiki Na Hana Kamuwa Da Muggan Cututtuka -WHO

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.