Mahaifiyar wata yarinya yar shekaru 8 da ake zargi jami’in hukumar daƙile sha da fataucin ƙwayoyi ta ƙasa (NDLEA) ya yi wa fyade a jihar Bauchi, ta nemi a yi musu adalci tare da nuna damuwa kan jinkirin tura wanda ake zargi kotu.
Uwar yarinyar, Salamatu Musa, wadda ke zaune a Dorawan Dillalai a Bauchi, ta shigar da ƙorafinta ne ta hanyar lauyanta na kare haƙƙin ɗan adam, Barrister Alkasim Mohammed na ƙungiyar ‘Organization for African Child Development and Human Rights Protection’.
Lauyan ya bayyana cewa lamarin ya auku ne a ranar 5 ga Yuli, 2026, lokacin da aka aiki yarinyar siyan ruwan leda a gidan makwabcinsu, Muhammad Mustapha Makama mai shekaru 45, wanda ma’aikacin NDLEA ne, inda ake zarginsa da yi mata fyade bayan ya yaudare ta.
Bayan shigar da ƙorafi a sahen ‘E’ na Rundunar ‘Yansandan Jihar Bauchi, ‘da yansanda sun kama Makama, amma ya shafe kusan makonni uku a tsare ba tare da an gurfanar da shi gaban kotu ba, lamarin da ya sa ƙungiyar rubuta takardar ƙorafi ga Kwamishinan ‘Yansanda na Jihar.
Kakakin rundunar ‘yansandan jihar Bauchi, SP Nafiu Habib, ya tabbatar da kama wanda ake zargin, inda ya ba da tabbacin cewa nan ba da daɗewa ba za a mika shi gaban kotu domin fuskantar shari’a.














