Dan takarar gwamnan Kano a jam’iyyar NNPP, Abba Kabir Yusuf ya bukaci jami’an tsaro da su sake saka ido sosai wajen ganin cewa an yi zabe lafiya.
Abba, ya bayyana haka ne a mazabarsa da ke uguwar Chiranci a karamar hukumar Gwale, bayan ya kada kuri’arsa.
- ‘Yansanda Sun Ceto Ma’aikatan INEC 19 Da Aka Sace A Imo
- Yadda Wakilan Jam’iyya Ke Siye Mutane Da Atamfa A Kano
Ya ce, ya zama dole jami’an tsaro su sake dagewa wajen ganin ba a samu hargitsi ba a lokacin zabe ba.
ADVERTISEMENT
Sannan ya jinjina wa jami’an tsaron bisa rawar da suke takawa wajen ganin an yi zaben lafiya an gama lafiya.
Abba, wanda ya yi takarar gwamnan Kano a karkashin jam’iyyar PDP a zaben 2019, ya ce jam’iyyarsa ta NNPP ce za ta samu nasara a wannan zaben.














