ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Yi Garkuwa Da Fiye Da Mutum 100 A Sakkwato

by Abubakar Abba
2 months ago
Garkuwa

Shugaban karamar hukumar Wurno a Jihar Sakkwato, Alhaji Abba Isa Sadik Achida, ya ce mazauna karamar hukumar na kara barin gidajensu a dare saboda karuwar yawaitar hare-haren ‘yan bindiga.

Ya ce yanayin ya zama babban damuwa ga mazauna yankin, gwamnatin jiha da ta tarayya, har ma da hukumomin tsaro sun kasa dakatar da hare-haren wanda a halin yanzu yana faruwa kusan kullum a wasu sassan karamar hukumar.

“Mutanen ba sa iya rufe idonsu biyu su yi bacci sosai,” in ji shi. Ya bayyana haka a yayin da yake magana da ‘yan jarida a Sakkwato.

ADVERTISEMENT

Shugaban karamar hukumar ya koka kan rayuka da dukiyoyin da suke salwanta sakamakon hare-haren ‘yan bindiga a cikin ‘yan shekarun nan. Ya kara da cewa sama da mazauna 100 a halin yanzu suna hannun ‘yan bindiga a fadin yankin.

Ya ce dubban mutane yanzu suna zuwa garin Achida kowace yamma don su kwana, sannan su dawo idan gari ya waye.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

“Suna kwana a makarantun firamare da duk wani wuri da aka samu. Ba za a iya kwatanta irin kalubalan da suke fuskanta kullum ba,” in ji shi.

Achida ya kuma nuna damuwa kan ayyukan wasu da ake zargin masu bayar da bayanai ne ga masu kai hari, amma ya lura cewa al’ummomi sun fara tallafa wa hukumomin tsaro da bayanan sirri yayin da suka kafa kungiyoyin farar hula masu gadin garin.

Ya ce ‘yan bindiga suna toshe manyan tituna da dare, musamman a ranakun kasuwa a Achida da Goronyo.

Yayin da yake yabo wa Gwamna Ahmed Aliyu kan kokarinsa na inganta tsaro, shugaban karamar hukumar ya yi kira da a kara daukar matakan gaggawa, ciki har da kafa sansanin soja a Achida.

Haka kuma ya bukaci a kirkiro karin rassan ‘yansanda a Achida da Kwargaba da Chacho da sauran yakuna da suke cikin hadari. Ya jaddada bukatar samun isassun ma’aikata da kayan aiki.

A cewarsa, karamar hukumar ta fara gyaran tashoshin ‘yansanda ta Achida.

A martaninsa, kwamishinan ‘yansandan Jihar Sakkwato, Hayatu Hassan Shaffa, ya ce rundunar tana sane da halin da ake ciki kuma tana kara kokari wajen magance lamarin.

“Ba mu dauki wannan matsala da sauki ba. Za a tura karin ma’aikata da kayan aiki don dawo da komai yadda aka saba,” in ji shi.

Ya tabbatar da cewa ‘yansanda ba za su yi kasa a gwiwa ba har sai dukkan sassan jihar sun kasance cikin aminci.

Rahotanni sun baya yadda wasu ‘yan bindiga suka kai hari garin Achida a ranar 17 ga Afrilu, suka kashe mutane biyu sannan suka sace wasu 23, ciki har da mata, yaro mai shekara 10 da masu tsaron gari.

Haka kuma a wani lamari, ‘yan bindiga sun kai hari garin Chacho awanni kafin aure, inda suka sace amarya, ‘yan mata masu daukar amarya da sauran mata tara.

Shugabannin al’umma sun ce Chacho ya samu rahoton kusan hare-hare 10 a cikin shekaru biyar da suka gabata, tare da kashe fiye da mazauna yanki 30.

Mazauna yankin sun bayyana Wurno a matsayin wuri mai yawan tashin hankali, inda mazauna yankin sau da yawa suke fuskantar matsaloli, yayin da karancin hanyar sadarwar waya ke jinkirta kiran neman agaji.

Sun yi kira a kafa sassanin sojoji da ‘yansanda na dindindin don magance hare-hare ‘yan bindiga.

Garkuwa
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Ko Barcelona Na Iya Lashe Gasar LaLiga A Yau?

Ko Barcelona Na Iya Lashe Gasar LaLiga A Yau?

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.