ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Yi Garkuwa Da Fiye Da Mutum 100 A Sakkwato

by Abubakar Abba
2 months ago
Garkuwa

Shugaban karamar hukumar Wurno a Jihar Sakkwato, Alhaji Abba Isa Sadik Achida, ya ce mazauna karamar hukumar na kara barin gidajensu a dare saboda karuwar yawaitar hare-haren ‘yan bindiga.

Ya ce yanayin ya zama babban damuwa ga mazauna yankin, gwamnatin jiha da ta tarayya, har ma da hukumomin tsaro sun kasa dakatar da hare-haren wanda a halin yanzu yana faruwa kusan kullum a wasu sassan karamar hukumar.

“Mutanen ba sa iya rufe idonsu biyu su yi bacci sosai,” in ji shi. Ya bayyana haka a yayin da yake magana da ‘yan jarida a Sakkwato.

ADVERTISEMENT

Shugaban karamar hukumar ya koka kan rayuka da dukiyoyin da suke salwanta sakamakon hare-haren ‘yan bindiga a cikin ‘yan shekarun nan. Ya kara da cewa sama da mazauna 100 a halin yanzu suna hannun ‘yan bindiga a fadin yankin.

Ya ce dubban mutane yanzu suna zuwa garin Achida kowace yamma don su kwana, sannan su dawo idan gari ya waye.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

“Suna kwana a makarantun firamare da duk wani wuri da aka samu. Ba za a iya kwatanta irin kalubalan da suke fuskanta kullum ba,” in ji shi.

Achida ya kuma nuna damuwa kan ayyukan wasu da ake zargin masu bayar da bayanai ne ga masu kai hari, amma ya lura cewa al’ummomi sun fara tallafa wa hukumomin tsaro da bayanan sirri yayin da suka kafa kungiyoyin farar hula masu gadin garin.

Ya ce ‘yan bindiga suna toshe manyan tituna da dare, musamman a ranakun kasuwa a Achida da Goronyo.

Yayin da yake yabo wa Gwamna Ahmed Aliyu kan kokarinsa na inganta tsaro, shugaban karamar hukumar ya yi kira da a kara daukar matakan gaggawa, ciki har da kafa sansanin soja a Achida.

Haka kuma ya bukaci a kirkiro karin rassan ‘yansanda a Achida da Kwargaba da Chacho da sauran yakuna da suke cikin hadari. Ya jaddada bukatar samun isassun ma’aikata da kayan aiki.

A cewarsa, karamar hukumar ta fara gyaran tashoshin ‘yansanda ta Achida.

A martaninsa, kwamishinan ‘yansandan Jihar Sakkwato, Hayatu Hassan Shaffa, ya ce rundunar tana sane da halin da ake ciki kuma tana kara kokari wajen magance lamarin.

“Ba mu dauki wannan matsala da sauki ba. Za a tura karin ma’aikata da kayan aiki don dawo da komai yadda aka saba,” in ji shi.

Ya tabbatar da cewa ‘yansanda ba za su yi kasa a gwiwa ba har sai dukkan sassan jihar sun kasance cikin aminci.

Rahotanni sun baya yadda wasu ‘yan bindiga suka kai hari garin Achida a ranar 17 ga Afrilu, suka kashe mutane biyu sannan suka sace wasu 23, ciki har da mata, yaro mai shekara 10 da masu tsaron gari.

Haka kuma a wani lamari, ‘yan bindiga sun kai hari garin Chacho awanni kafin aure, inda suka sace amarya, ‘yan mata masu daukar amarya da sauran mata tara.

Shugabannin al’umma sun ce Chacho ya samu rahoton kusan hare-hare 10 a cikin shekaru biyar da suka gabata, tare da kashe fiye da mazauna yanki 30.

Mazauna yankin sun bayyana Wurno a matsayin wuri mai yawan tashin hankali, inda mazauna yankin sau da yawa suke fuskantar matsaloli, yayin da karancin hanyar sadarwar waya ke jinkirta kiran neman agaji.

Sun yi kira a kafa sassanin sojoji da ‘yansanda na dindindin don magance hare-hare ‘yan bindiga.

Garkuwa
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Ko Barcelona Na Iya Lashe Gasar LaLiga A Yau?

Ko Barcelona Na Iya Lashe Gasar LaLiga A Yau?

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.