ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Yi Garkuwa Da Fiye Da Mutum 100 A Sakkwato

by Abubakar Abba
1 month ago
Garkuwa

Shugaban karamar hukumar Wurno a Jihar Sakkwato, Alhaji Abba Isa Sadik Achida, ya ce mazauna karamar hukumar na kara barin gidajensu a dare saboda karuwar yawaitar hare-haren ‘yan bindiga.

Ya ce yanayin ya zama babban damuwa ga mazauna yankin, gwamnatin jiha da ta tarayya, har ma da hukumomin tsaro sun kasa dakatar da hare-haren wanda a halin yanzu yana faruwa kusan kullum a wasu sassan karamar hukumar.

“Mutanen ba sa iya rufe idonsu biyu su yi bacci sosai,” in ji shi. Ya bayyana haka a yayin da yake magana da ‘yan jarida a Sakkwato.

ADVERTISEMENT

Shugaban karamar hukumar ya koka kan rayuka da dukiyoyin da suke salwanta sakamakon hare-haren ‘yan bindiga a cikin ‘yan shekarun nan. Ya kara da cewa sama da mazauna 100 a halin yanzu suna hannun ‘yan bindiga a fadin yankin.

Ya ce dubban mutane yanzu suna zuwa garin Achida kowace yamma don su kwana, sannan su dawo idan gari ya waye.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

“Suna kwana a makarantun firamare da duk wani wuri da aka samu. Ba za a iya kwatanta irin kalubalan da suke fuskanta kullum ba,” in ji shi.

Achida ya kuma nuna damuwa kan ayyukan wasu da ake zargin masu bayar da bayanai ne ga masu kai hari, amma ya lura cewa al’ummomi sun fara tallafa wa hukumomin tsaro da bayanan sirri yayin da suka kafa kungiyoyin farar hula masu gadin garin.

Ya ce ‘yan bindiga suna toshe manyan tituna da dare, musamman a ranakun kasuwa a Achida da Goronyo.

Yayin da yake yabo wa Gwamna Ahmed Aliyu kan kokarinsa na inganta tsaro, shugaban karamar hukumar ya yi kira da a kara daukar matakan gaggawa, ciki har da kafa sansanin soja a Achida.

Haka kuma ya bukaci a kirkiro karin rassan ‘yansanda a Achida da Kwargaba da Chacho da sauran yakuna da suke cikin hadari. Ya jaddada bukatar samun isassun ma’aikata da kayan aiki.

A cewarsa, karamar hukumar ta fara gyaran tashoshin ‘yansanda ta Achida.

A martaninsa, kwamishinan ‘yansandan Jihar Sakkwato, Hayatu Hassan Shaffa, ya ce rundunar tana sane da halin da ake ciki kuma tana kara kokari wajen magance lamarin.

“Ba mu dauki wannan matsala da sauki ba. Za a tura karin ma’aikata da kayan aiki don dawo da komai yadda aka saba,” in ji shi.

Ya tabbatar da cewa ‘yansanda ba za su yi kasa a gwiwa ba har sai dukkan sassan jihar sun kasance cikin aminci.

Rahotanni sun baya yadda wasu ‘yan bindiga suka kai hari garin Achida a ranar 17 ga Afrilu, suka kashe mutane biyu sannan suka sace wasu 23, ciki har da mata, yaro mai shekara 10 da masu tsaron gari.

Haka kuma a wani lamari, ‘yan bindiga sun kai hari garin Chacho awanni kafin aure, inda suka sace amarya, ‘yan mata masu daukar amarya da sauran mata tara.

Shugabannin al’umma sun ce Chacho ya samu rahoton kusan hare-hare 10 a cikin shekaru biyar da suka gabata, tare da kashe fiye da mazauna yanki 30.

Mazauna yankin sun bayyana Wurno a matsayin wuri mai yawan tashin hankali, inda mazauna yankin sau da yawa suke fuskantar matsaloli, yayin da karancin hanyar sadarwar waya ke jinkirta kiran neman agaji.

Sun yi kira a kafa sassanin sojoji da ‘yansanda na dindindin don magance hare-hare ‘yan bindiga.

Garkuwa
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Ko Barcelona Na Iya Lashe Gasar LaLiga A Yau?

Ko Barcelona Na Iya Lashe Gasar LaLiga A Yau?

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.