Shugaban karamar hukumar Wurno a Jihar Sakkwato, Alhaji Abba Isa Sadik Achida, ya ce mazauna karamar hukumar na kara barin gidajensu a dare saboda karuwar yawaitar hare-haren ‘yan bindiga.
Ya ce yanayin ya zama babban damuwa ga mazauna yankin, gwamnatin jiha da ta tarayya, har ma da hukumomin tsaro sun kasa dakatar da hare-haren wanda a halin yanzu yana faruwa kusan kullum a wasu sassan karamar hukumar.
“Mutanen ba sa iya rufe idonsu biyu su yi bacci sosai,” in ji shi. Ya bayyana haka a yayin da yake magana da ‘yan jarida a Sakkwato.
Shugaban karamar hukumar ya koka kan rayuka da dukiyoyin da suke salwanta sakamakon hare-haren ‘yan bindiga a cikin ‘yan shekarun nan. Ya kara da cewa sama da mazauna 100 a halin yanzu suna hannun ‘yan bindiga a fadin yankin.
Ya ce dubban mutane yanzu suna zuwa garin Achida kowace yamma don su kwana, sannan su dawo idan gari ya waye.
“Suna kwana a makarantun firamare da duk wani wuri da aka samu. Ba za a iya kwatanta irin kalubalan da suke fuskanta kullum ba,” in ji shi.
Achida ya kuma nuna damuwa kan ayyukan wasu da ake zargin masu bayar da bayanai ne ga masu kai hari, amma ya lura cewa al’ummomi sun fara tallafa wa hukumomin tsaro da bayanan sirri yayin da suka kafa kungiyoyin farar hula masu gadin garin.
Ya ce ‘yan bindiga suna toshe manyan tituna da dare, musamman a ranakun kasuwa a Achida da Goronyo.
Yayin da yake yabo wa Gwamna Ahmed Aliyu kan kokarinsa na inganta tsaro, shugaban karamar hukumar ya yi kira da a kara daukar matakan gaggawa, ciki har da kafa sansanin soja a Achida.
Haka kuma ya bukaci a kirkiro karin rassan ‘yansanda a Achida da Kwargaba da Chacho da sauran yakuna da suke cikin hadari. Ya jaddada bukatar samun isassun ma’aikata da kayan aiki.
A cewarsa, karamar hukumar ta fara gyaran tashoshin ‘yansanda ta Achida.
A martaninsa, kwamishinan ‘yansandan Jihar Sakkwato, Hayatu Hassan Shaffa, ya ce rundunar tana sane da halin da ake ciki kuma tana kara kokari wajen magance lamarin.
“Ba mu dauki wannan matsala da sauki ba. Za a tura karin ma’aikata da kayan aiki don dawo da komai yadda aka saba,” in ji shi.
Ya tabbatar da cewa ‘yansanda ba za su yi kasa a gwiwa ba har sai dukkan sassan jihar sun kasance cikin aminci.
Rahotanni sun baya yadda wasu ‘yan bindiga suka kai hari garin Achida a ranar 17 ga Afrilu, suka kashe mutane biyu sannan suka sace wasu 23, ciki har da mata, yaro mai shekara 10 da masu tsaron gari.
Haka kuma a wani lamari, ‘yan bindiga sun kai hari garin Chacho awanni kafin aure, inda suka sace amarya, ‘yan mata masu daukar amarya da sauran mata tara.
Shugabannin al’umma sun ce Chacho ya samu rahoton kusan hare-hare 10 a cikin shekaru biyar da suka gabata, tare da kashe fiye da mazauna yanki 30.
Mazauna yankin sun bayyana Wurno a matsayin wuri mai yawan tashin hankali, inda mazauna yankin sau da yawa suke fuskantar matsaloli, yayin da karancin hanyar sadarwar waya ke jinkirta kiran neman agaji.
Sun yi kira a kafa sassanin sojoji da ‘yansanda na dindindin don magance hare-hare ‘yan bindiga.















Discussion about this post