ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Fasahar ‘HereafterAI’ Ke Ba Da Damar Magana Da Muryar Mutum Bayan Mutuwarsa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
HereafterAI

A shekarar 2016 ce, James Blahos ya samu wani mummunan labarin cewar an gano mahaifinsa na fama da cutar sankara, wadda ta riga ta yi muni.

James, wanda ke zaune a garin Oakland, a Jihar California na kasar Amurka ya ce, “Ina matukar son mahaifina, ga shi zan rasa shi.” Ya sha alwashin amfani da sauran lokacin da ya rage wa mahaifin nasa na rayuwa yadda ya kamata.

  • ‘Yancin Kananan Hukumomi: Kotun Koli Ta Bai Wa Jihohi 36 Kwana 7 Su Kare Kansu
  • Li Qiang Ya Yi Kira Ga Sin Da Equatorial Guinea Da Su Kare Moriyar Bai Daya Ta Kasashe Masu Tasowa

“Na zauna tare da shi, inda ya ba ni tarihin rayuwarsa, na kwashe sa’o’i ina nadar tarihinsa da yake ba ni da kansa.”

ADVERTISEMENT

Lamarin ya zo daidai lokacin da James ke kokarin shiga harkar ci gaban zamani ta kirkirarriyar basira (AI) daga nan ne ya fara aikinsa.

“Sai na yi tunanin me zai hana na yi wani abu da wannan lokaci da na samu?. Domin na samu abun da zan rika tunawa da shi da kuma jin tamkar yana tare da ni.”

LABARAI MASU NASABA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Mahaifin James ya rasu a shekarar 2017, dab da lokacin da James din ya samar da manhajar kirkirarriyar basira wadda ke amsa tambayoyi kan rayuwar mahaifin nasa cikin muryarsa.

Masana kimiyya sun dade su na hasashen yadda za a iya ci gaba da amfani da wasu abubuwa na mutanen da suka mutu, to a yanzu ci gaban harkar fasasha ya sa mafarkin nasu ya zama gaskiya.

A 2019, James ya mayar da abin da ya kirkira zuwa wata manhaja wadda ya rada wa suna ‘HereafterAI’, wato kirkirarriyar basirar bayan mutuwa, wadda ke bai wa duk mai bukata damar nada tare da amfani da muryar ‘yan’uwansu ko bayan sun mutu, kamar yadda BBC ta nakalto.

Ya ce duk da cewa manhajar ba za ta cire masa damuwar rashin mahaifinsa ba, amma ta samar masa abun da ba zai iya samu ba in da bai yi hakan ba.

Yayin da manhajar ‘HereafterAI’ ke bai wa masu amfani da ita damar sanya hoton ‘yan’uwansu da suke so su fito a kan waya ko kwamfuta a lokacin da suke amfani da manhajar, wani kamfanin kirkirarriyar basirar ya kara inganta lamarin.

Wani kamfanin sadarwar zamani da kirkirarriyar basira a Koriya ta Kudu mai suna DeepBrain AI, yana samar da kwafin mutum (Abatar) bayan daukar murya da bidiyon mutum na sa’o’i ta yadda zai dauki yanayin motsin fuskar mutum da sauka da tashin muryarsu.

“Mukan samar da tamka ta surar mutum da kimanin kashi 96.,” in ji Michael Jung, shugaban sashen kudi na kamfanin DeepBrians AI.

Ya kara da cewa “Ta yadda iyalan mamaci ba za su ji wani iri ba idan suna tattaunawa da hoton nasa, duk kuwa da cewa ba na gaske ba ne.”

Kamfanin na da yakinin cewa wannan ci gaba ta fasaha za ta zamo wani bangare na abin da ya shafi mace-mace, “Inda za mu iya shiryawa kafin lokacin mutuwa, ta yadda za mu bar wani abu da za a ci gaba da tunawa da mu har abada.”

Tsarin yana da tsada, kuma ba kowa ne ke iya kirkirar kwafen dan uwansa ba, kamfanin ne ke yi.
Dangi kan biya kamfanin kudin da suka kai dalar Amurka 50,000 domin su aikin nadar bidiyon ‘yan’uwan nasu da kuma yin kwafen.

Duk da tsadar abin, wasu masu zuba jari na da yakinin cewa mutane za su karbi tsarin, har ma kamfanin na DeepBrain ya tara kudi dalar Amurka miliyan 44 a gidauniyar da ya kafa.

Sai dai wata kwararriya kan halayyar Dan’adam, Laberne Antrobus ta ce ya kamata a yi taka-tsantsan wajen amfani da irin wannan fasaha a lokacin da mutane ke cikin jimami.

“Rashin wani namu abu ne da ke girgiza mutum, ka da ya zama sai ka ni kamar ka kusa komawa daidai amma wani abu ya sake mayar da kai.

“Tunanin cewa za ka samu damar jin muryar wani naka da ya rasu ko kuma ka ji su suna magana lamari ne da zai iya sanya mutum cikin rudani.”

Antrobus ta kara da cewa ka da mutane su gaggauta rungumar wannan fasaha ta yin magana da kwafen dan’uwansu da suka mutu. “Dole ne ka zama mai karfin rai kafin ka gwada yin haka. A bi abubuwa a hankali.”

HereafterAI
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

February 21, 2026
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

April 19, 2025
Next Post
Sin Da Kasashen Larabawa Za Su Gaggauta Aikin Kafa Al’umma Mai Makomar Bai Daya

Sin Da Kasashen Larabawa Za Su Gaggauta Aikin Kafa Al’umma Mai Makomar Bai Daya

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.