ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

by Abubakar Abba and Sulaiman
1 hour ago
Abinci

A yayin da kakar noman 2026 ta fara kankama, Gwamnatin Jihar Kano, ta bullo da wasu sabbin samarwa fannin aikin noman jihar matakai.

Manufar ita ce, don ta ƙara ƙarfafa wa manoman jihar guiwa, musamman duba da hauhawar farashin kayan abinci da kuma tsadar kayan aikin noma.

Kazalika, gwamnatin ta kuma zuba jari a bangaren noman rani, ta hanyar samar da kayan aiki na zamani da ƙirƙiro da shirye-shiyen da za su taimaka wa manoman jihar, domin samar da gurbi mai yawa.

ADVERTISEMENT

Ya zuwa yanzu, gwamnatin ta samu nasarar kusan kashi 80 cikin ɗari, na burin da take son cimma a fannin.

Kano dai, ta dogara ne kacoka, kan aikin noma wajen ƙara bunƙasa tattalin arziƙinta, musamman domin samar da wadataccen abinci da yaƙar talauci da ƙara ƙarfafa tattalin arziƙin mazauna karkara.

LABARAI MASU NASABA

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Kwamishinan Ma’aiktar Aikin Noma da Kula da Albarkatun Ƙasa, Dakta Yakubu Ɗanjuma Mahmud, ya danganta wannan nasarar kan samar da kyawawan tsare-tsare a ƙarƙashin gwamnatin Abba Kabir Yusuf, tun bayan ɗare karagar shugabancin jihar a 2023.

A cewarsa, ɗaya daga cikin matakan da gwamnatin ta ɗauka, su ne; tattara bayanan manoman jihar, domin yin amfani da su wajen samar da tsarin inganta fannin.

Wasu daga cikin nasarorin da gwamnatin ta samar a cewarsa, sun haɗa da sake farfaɗo da noman rani a ɗaukacin faɗin jihar.

“Mun maido tare da kuma gyara kadadar noma 1,230 da kuma ƙasar yin noma a jihar, tare da dawo da wajen yin noman rani da ke Kadawa,” a cewar Mahmud.

Ya ƙara da cewa, gwamnatin ta ɗauki matakan daƙile yawan samun rikici a tsakanin manoma da Fulani Makiyaya da ke jihar, musamman ta hanyar katange kimanin Buratalai masu tsawon kilo mita 1,300.

A cewarsa, yanzu haka, gwamnatin na shirin fara wani babban aiki na gina Dam a dajin Ɗantsoshiya, wanda ya kai mai kimanin, tsawon kilo mita biyu da za a iya tara ruwan da zai kai lita miliyan uku.

“Dam ɗin zai taimaka wajen samar da ruwa ga kimain kadada 1,250, idan aka kammala aikin,” in ji Kwamishinan.

Ya ci gaba da cewa, gwamnatin ta kuma gina ƙananan Dam 11 a yankunan Albasu, Shanono, Gari, Dawakin Kudu, Rogo, Ajingi da kuma Bichi.

Mahmud ya ce, waɗannan Dam-dam ɗin, za su iya wadata kadadar noma kimanin 1,200, waɗanda kuma ake sa ran za su karaɗe kimanin kadada 2,000.

“A yanzu haka, akwai kuma wasu sabbin kimanin kadadar noman rani 2,000 da aka tsara za a samar a wasu yankunan jihar,” in ji Mahmud.

Ya ƙara da cewa, gwamnatin ta kuma samar da kayan aiki ga manoman jihar, inda ya ce; a shekaru uku na hawan gwamnatin, jihar ta samar da Tirelolin takin zamani sama da 623 ga manoman jihar.

Noma
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Hukumar NEPZA Ta Tabbatar Wa Da Masu Zuba Jari Goyon Bayanta
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur
Noma
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
  • Sulaiman
    Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin
  • Sulaiman
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

MASU ALAKA

Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
Noma Da Kiwo

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

June 12, 2026
Next Post
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026
Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

June 19, 2026
Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.