ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

by Abubakar Abba and Sulaiman
3 weeks ago
Abinci

A yayin da kakar noman 2026 ta fara kankama, Gwamnatin Jihar Kano, ta bullo da wasu sabbin samarwa fannin aikin noman jihar matakai.

Manufar ita ce, don ta ƙara ƙarfafa wa manoman jihar guiwa, musamman duba da hauhawar farashin kayan abinci da kuma tsadar kayan aikin noma.

Kazalika, gwamnatin ta kuma zuba jari a bangaren noman rani, ta hanyar samar da kayan aiki na zamani da ƙirƙiro da shirye-shiyen da za su taimaka wa manoman jihar, domin samar da gurbi mai yawa.

ADVERTISEMENT

Ya zuwa yanzu, gwamnatin ta samu nasarar kusan kashi 80 cikin ɗari, na burin da take son cimma a fannin.

Kano dai, ta dogara ne kacoka, kan aikin noma wajen ƙara bunƙasa tattalin arziƙinta, musamman domin samar da wadataccen abinci da yaƙar talauci da ƙara ƙarfafa tattalin arziƙin mazauna karkara.

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

Kwamishinan Ma’aiktar Aikin Noma da Kula da Albarkatun Ƙasa, Dakta Yakubu Ɗanjuma Mahmud, ya danganta wannan nasarar kan samar da kyawawan tsare-tsare a ƙarƙashin gwamnatin Abba Kabir Yusuf, tun bayan ɗare karagar shugabancin jihar a 2023.

A cewarsa, ɗaya daga cikin matakan da gwamnatin ta ɗauka, su ne; tattara bayanan manoman jihar, domin yin amfani da su wajen samar da tsarin inganta fannin.

Wasu daga cikin nasarorin da gwamnatin ta samar a cewarsa, sun haɗa da sake farfaɗo da noman rani a ɗaukacin faɗin jihar.

“Mun maido tare da kuma gyara kadadar noma 1,230 da kuma ƙasar yin noma a jihar, tare da dawo da wajen yin noman rani da ke Kadawa,” a cewar Mahmud.

Ya ƙara da cewa, gwamnatin ta ɗauki matakan daƙile yawan samun rikici a tsakanin manoma da Fulani Makiyaya da ke jihar, musamman ta hanyar katange kimanin Buratalai masu tsawon kilo mita 1,300.

A cewarsa, yanzu haka, gwamnatin na shirin fara wani babban aiki na gina Dam a dajin Ɗantsoshiya, wanda ya kai mai kimanin, tsawon kilo mita biyu da za a iya tara ruwan da zai kai lita miliyan uku.

“Dam ɗin zai taimaka wajen samar da ruwa ga kimain kadada 1,250, idan aka kammala aikin,” in ji Kwamishinan.

Ya ci gaba da cewa, gwamnatin ta kuma gina ƙananan Dam 11 a yankunan Albasu, Shanono, Gari, Dawakin Kudu, Rogo, Ajingi da kuma Bichi.

Mahmud ya ce, waɗannan Dam-dam ɗin, za su iya wadata kadadar noma kimanin 1,200, waɗanda kuma ake sa ran za su karaɗe kimanin kadada 2,000.

“A yanzu haka, akwai kuma wasu sabbin kimanin kadadar noman rani 2,000 da aka tsara za a samar a wasu yankunan jihar,” in ji Mahmud.

Ya ƙara da cewa, gwamnatin ta kuma samar da kayan aiki ga manoman jihar, inda ya ce; a shekaru uku na hawan gwamnatin, jihar ta samar da Tirelolin takin zamani sama da 623 ga manoman jihar.

Noma
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Matatar Ɗangote Ta Ƙaryata Iƙirarin Dillalan Man Fetur 
Noma
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni
  • Sulaiman
    ‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda
  • Sulaiman
    Taron Intanet Na Sin Karo Na 25 Ya Bayyana Yadda Ake Amfani Da Fasahar AI A Rayuwar Yau Da Kullum
  • Sulaiman
    Tunanin Xi Jinping kan JKS: Hikimar Mulki Ta Farfado Da Kasa Da Kuma Tasirinta A Duniya

MASU ALAKA

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 
Noma Da Kiwo

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
Next Post
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

LABARAI MASU NASABA

Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni

Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni

July 9, 2026
‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda

‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda

July 9, 2026
Taron Intanet Na Sin Karo Na 25 Ya Bayyana Yadda Ake Amfani Da Fasahar AI A Rayuwar Yau Da Kullum

Taron Intanet Na Sin Karo Na 25 Ya Bayyana Yadda Ake Amfani Da Fasahar AI A Rayuwar Yau Da Kullum

July 9, 2026
Tunanin Xi Jinping kan JKS: Hikimar Mulki Ta Farfado Da Kasa Da Kuma Tasirinta A Duniya

Tunanin Xi Jinping kan JKS: Hikimar Mulki Ta Farfado Da Kasa Da Kuma Tasirinta A Duniya

July 9, 2026
Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

July 9, 2026
Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Kasar Sin Na Kara Samun Tagomashi A Kasuwannin Duniya

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Kasar Sin Na Kara Samun Tagomashi A Kasuwannin Duniya

July 9, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ɗaga Albashin Sojoji Daga Naira 49,000 Zuwa Naira 100,000 – Ministan Tsaro

Gwamnatin Tarayya Ta Ɗaga Albashin Sojoji Daga Naira 49,000 Zuwa Naira 100,000 – Ministan Tsaro

July 9, 2026
An Gabatar Da Shirin Fadar Potala Ta Kafar CMG

An Gabatar Da Shirin Fadar Potala Ta Kafar CMG

July 9, 2026
kebbi

Makarantu Za Su Ci Gaba Da Zama A Rufe Har Sai Yanayin Tsaro Ya Inganta – Gwamnatin Kebbi

July 9, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Shugabar Namibia

Li Qiang Ya Gana Da Shugabar Namibia

July 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.