A makon da ya gabata, Gwamna Mai Mala Buni ya je kasar Chad, inda ya ziyarci ‘yan gudun hijirar Nijeriya a Kaya da ke Lardin Lac. A bayyane yake, Gwamnan Jihar Yobe ya kasance jakadan diflomasiyya, wakilin tsaro na kasa, da kuma masani a harkokin ci gaba.
Yayin da yake alkawarin taimaka wa ‘yan gudun hijira su koma gida, Buni wanda yake tare da kwamandan rundunar hadin gwiwar sojojin kasashen daban-daban, Manjo Janar Saidu Tanko Audu, shi ne jami’in Nijeriya guda daya tilo da ya ziyarci ‘yan gudun hijirar tun lokacin da aka kafa sansani a wurin.
A watan Yunin 2025, Buni ya ziyarci Chadi, inda ya jagoranci taron farko na kwamitin Tafkin Chadi. Amma ba shi kadai ba ne gwamnan arewa maso gabas da ke shiga kasashen makwabta a yankin Tafkin Chadi.
Kokarin kiyaye zaman lafiya ya hada har da hada kai tsakanin kananan kasashe a fadin iyakoki. Haka kuma kokarin mayar da ‘yan gudun hijira gida shi ma alama ce cewa matsin lamba daga Boko Haram da sauran kungiyoyi ya ragu.
Zulum ya ziyarci Nijar a watan Oktoba, 2025, kuma ya fara wata ziyara Kamaru a watan Disamba 2025. Zulum ya yi watanni yana kokarin dawo da ‘yan gudun hijira ‘yan asalin Jihar Borno, wadanda a wasu lokuta suka makale a Jamhuriyar Nijar, Chadi, ko Kamaru na tsawon shekaru goma.
Ko da yake shi ba mamba na kungiyar ba ne, Gwamnan Jihar Taraba, Agbu Kefas ya ketare iyaka zuwa Kamaru tare da wata tawaga da ta hada da ‘yan majalisa da jami’an tsaro domin karfafa hadin gwiwa kan yaki da ta’addanci da laifuka a kan iyaka.
Amma akwai wani abu da ya hada dukkan ziyarorinsu na ketare. Duk gwamnonin sun hadu da abokan aikinsu a kasashe daban-daban. Haka nan akai-akai suna tare da jami’an leken asiri da jami’an tsaro. Akwai dalili hakan.
Bayan radanin dangantakar diflomasiyya tsakanin Nijeriya da Jamhuriyar Nijar, Burkina Faso, da Mali a gefe guda, da kuma korar sojojin Faransa daga wasu kasashen a yammacin Afirka, aikin hadin tsaro ya kara tsananta.
Kungiyar gwamnonin Tafkin Chadi, sun fara taka muhimmiyar rawa wajen tsara harkokin tsaro da tattalin arziki a iyakokin kasashe. Rundunar hadin gwiwar sojoji ta kasashen daban-daban ma ta samu yin wasu gyare-gyare.
Lokacin da aka kafa kungiyar a 2018, mafi yawanci ya nuna yabo kan kokarin gwamnatin tarayya wajen tsara tsaro, ci gaba, da taimakon ‘yan gudun hijira.
Kungiyar tana da gwamnonin takwas a matsayin mambobi, uku daga cikinsu na arewa maso gabashin Nijeriya ne, biyu daga Chadi, biyu daga Kamaru, daya kuma daga Jamhuriyar Nijar.
Gwamnonin Nijeriya uku, Babagana Zulum na Borno, Adamu Fintiri na Adamawa, da Mai Mala Buni na Yobe wanda kuma shi ne shugaban kungiyar, suna kara zama manyan jami’an Nijeriya wajen aiwatar da manufofin tsaron kasa a yankin Tafkin Chadi.
Sai dai wajen halartar taron kungiyar a watan Janairu 2025 a Maiduguri, Jihar Borno, Gwamnan Jihar Adamawa, Fintiri shi ne mafi karancin yin aiki. Amma a karshe, gwamnonin da ke gefen Tafkin Chadi sun cike wani gibi da cibiyoyin manufofin kasashen waje na Nijeriya suka bari.














