ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buni Ya Nuna Kwarewarsa Ta Diflomasiyya

by Shuaibu Shuaibu
2 weeks ago
Buni

A makon da ya gabata, Gwamna Mai Mala Buni ya je kasar Chad, inda ya ziyarci ‘yan gudun hijirar Nijeriya a Kaya da ke Lardin Lac. A bayyane yake, Gwamnan Jihar Yobe ya kasance jakadan diflomasiyya, wakilin tsaro na kasa, da kuma masani a harkokin ci gaba.

Yayin da yake alkawarin taimaka wa ‘yan gudun hijira su koma gida, Buni wanda yake tare da kwamandan rundunar hadin gwiwar sojojin kasashen daban-daban, Manjo Janar Saidu Tanko Audu, shi ne jami’in Nijeriya guda daya tilo da ya ziyarci ‘yan gudun hijirar tun lokacin da aka kafa sansani a wurin.

A watan Yunin 2025, Buni ya ziyarci Chadi, inda ya jagoranci taron farko na kwamitin Tafkin Chadi. Amma ba shi kadai ba ne gwamnan arewa maso gabas da ke shiga kasashen makwabta a yankin Tafkin Chadi.

ADVERTISEMENT

Kokarin kiyaye zaman lafiya ya hada har da hada kai tsakanin kananan kasashe a fadin iyakoki. Haka kuma kokarin mayar da ‘yan gudun hijira gida shi ma alama ce cewa matsin lamba daga Boko Haram da sauran kungiyoyi ya ragu.

Zulum ya ziyarci Nijar a watan Oktoba, 2025, kuma ya fara wata ziyara Kamaru a watan Disamba 2025. Zulum ya yi watanni yana kokarin dawo da ‘yan gudun hijira ‘yan asalin Jihar Borno, wadanda a wasu lokuta suka makale a Jamhuriyar Nijar, Chadi, ko Kamaru na tsawon shekaru goma.

LABARAI MASU NASABA

Shin Tinubu Ya Tabbatar Da Sauke Ribadu Daga Mukaminsa?

Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya

Ko da yake shi ba mamba na kungiyar ba ne, Gwamnan Jihar Taraba, Agbu Kefas ya ketare iyaka zuwa Kamaru tare da wata tawaga da ta hada da ‘yan majalisa da jami’an tsaro domin karfafa hadin gwiwa kan yaki da ta’addanci da laifuka a kan iyaka.

Amma akwai wani abu da ya hada dukkan ziyarorinsu na ketare. Duk gwamnonin sun hadu da abokan aikinsu a kasashe daban-daban. Haka nan akai-akai suna tare da jami’an leken asiri da jami’an tsaro. Akwai dalili hakan.

Bayan radanin dangantakar diflomasiyya tsakanin Nijeriya da Jamhuriyar Nijar, Burkina Faso, da Mali a gefe guda, da kuma korar sojojin Faransa daga wasu kasashen a yammacin Afirka, aikin hadin tsaro ya kara tsananta.

Kungiyar gwamnonin Tafkin Chadi, sun fara taka muhimmiyar rawa wajen tsara harkokin tsaro da tattalin arziki a iyakokin kasashe. Rundunar hadin gwiwar sojoji ta kasashen daban-daban ma ta samu yin wasu gyare-gyare.

Lokacin da aka kafa kungiyar a 2018, mafi yawanci ya nuna yabo kan kokarin gwamnatin tarayya wajen tsara tsaro, ci gaba, da taimakon ‘yan gudun hijira.

Kungiyar tana da gwamnonin takwas a matsayin mambobi, uku daga cikinsu na arewa maso gabashin Nijeriya ne, biyu daga Chadi, biyu daga Kamaru, daya kuma daga Jamhuriyar Nijar.

Gwamnonin Nijeriya uku, Babagana Zulum na Borno, Adamu Fintiri na Adamawa, da Mai Mala Buni na Yobe wanda kuma shi ne shugaban kungiyar, suna kara zama manyan jami’an Nijeriya wajen aiwatar da manufofin tsaron kasa a yankin Tafkin Chadi.

Sai dai wajen halartar taron kungiyar a watan Janairu 2025 a Maiduguri, Jihar Borno, Gwamnan Jihar Adamawa, Fintiri shi ne mafi karancin yin aiki. Amma a karshe, gwamnonin da ke gefen Tafkin Chadi sun cike wani gibi da cibiyoyin manufofin kasashen waje na Nijeriya suka bari.

Buni
Shuaibu Shuaibu
+ postsBio
  • Shuaibu Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/shuaibu-shuaibu/
    Shin Tinubu Ya Tabbatar Da Sauke Ribadu Daga Mukaminsa?
  • Shuaibu Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/shuaibu-shuaibu/
    Akwai Ayar Tabaya Kan Zuba Hannun Jarin Dala Miliyan 750 Na Yari
  • Shuaibu Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/shuaibu-shuaibu/
    Wa Tanimu Turaki Ke Fafutukar Karewa?
  • Shuaibu Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/shuaibu-shuaibu/
    Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya

MASU ALAKA

An Kusa Ceto Ɗaliban Neja Da Aka Sace – Ribadu
Bakon Marubuci

Shin Tinubu Ya Tabbatar Da Sauke Ribadu Daga Mukaminsa?

August 28, 2026
Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya
Bakon Marubuci

Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya

July 24, 2026
Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta
Bakon Marubuci

Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta

July 24, 2026
Next Post
Buni

Ƴansanda Sun Bankaɗo Kayan Wutar Lantarki Da Aka Sace A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.