Makonni biyu kenan da sace ɗalibai da ma’aikatan Makarantar Katolika ta St Mary, Papiri, a yankin ƙaramar hukumar Agwara ta Jihar Neja, amma jami’an makarantar sun ce, har yanzu masu satar ba su tuntuɓe su ba.
LEADERSHIP ta rahoto cewa, masu satar da ake zargin ‘yan bindiga ne sun kai hari makarantar a ranar 21 ga Nuwamba na wannan shekarar inda suka sace yara 315 da ma’aikata, amma yara 50 sun sami damar tserewa ‘yan kwanaki bayan sace su.
- An Jinjina Wa Shugaban NPA Kan Rage Cunkoso A Tashar Apapa
- Jakadan Sin Ya Gana Da Shugaba Tinubu, Inda Ya Jaddada Alkawarin Sin Na Karfafa Alaka Da Nijeriya
Shugaban makarantar ta Kontagora, ya tabbatar wa manema labarai cewa, “ɗalibai 265 da ma’aikata har yanzu suna tsare a wurin ‘yan bindigar kuma basu tuntuɓe mu ba.”
Sai dai, shugaban ya ce suna fatan tabbacin da tawagar gwamnatin tarayya ta bayar a karkashin jagorancin Mai Ba da Shawara kan Tsaron Kasa (NSA), Nuhu Ribadu, wanda ya ziyarci cocin a makon da ya gabata ya ba da tabbacin cewa yaran suna cikin koshin lafiya kuma za a ceto su nan ba da jimawa ba.














