ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Muka Sanya Tinubu Ya Soke Kwangilar Aikin Hanyar Kankara Zuwa Katsina inji Ibrahim Masari 

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
Tinubu

Baban mai taimakawa shugaban ƙasa akan harkokin siyasa Hon. Ibrahim Kabir Masari ya bayyana dalilan da yasa suka shiga suka fita shi da gwamna Dikko Raɗɗa a kasoke aikin sake gina hanyar kankara zuwa Katsina daga hannun ɗan kwangilar.

Ibrahim Kabir Masari ya yi wannan kalamai ne a Katsina a lokacin bikin raba shinkafar da gwamnatin tarayya ta baiwa jihar Katsina domin rabawa al’umma su rage raɗaɗin rayuwa da ake fama da shi.

  • Tinubu Zai Wuce Faransa Daga Birtaniya
  • Yadda Muka Sanya Tinubu Ya Soke Kwangilar Aikin Hanyar Kankara Zuwa Katsina – Ibrahim Masari 

Wannan aikin hanyar mai tsawon kilo mita 170 da ta taso daga marabar kankara zuwa Katsina ta haɗa ƙananan hukumomi bakwai da yawansu manoma ne sannan suna fuskantar matsalar tsaro daga ‘yan bindiga

ADVERTISEMENT

Kamar yadda alkaluma suka nuna aikin wannan hanya sai ratsa kananan hukumomi guda 7 da suka haɗa da Malumfashi da Kankara da Ɗanmusa da Safana da Dutsinma da Kurfi da kuma Ɓatagarawa a jihar Katsina.

Lokaci da aka bada aikin wannan hanya al’umma da dama sun nuna farin cikin su da samun wannan aiki wanda suka bayyana cewa zai taimakawa al’umma musamman manoma sannan zai taimakawa jami’an tsaro wajen kai ɗauki a ya yin da aka kai hari wuce gona da iri.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

Sai dai kwatsam aka ji labarin ministan ayyuka na Najeriya ya soke wannan kwangila daga hannun kamfanin da aka baiwa ita daga farko duk da cewa an fara aikin.

Shima a nasa jawabin baban mai taimakawa shugaban kasa a harkokin siyasa Hon Ibrahim Masari ya bayyana wasu hanyoyi da gwamnatin tarayya ta bada aikin su, sai dai ya ce hanyar kankara zuwa Katsina ba a ɗora ƙwarya a gurbin ta ba shi yasa suke je wajen shugaban ƙasa domin ya soke ta.

Ana dai zargin cewa wani jigo ne a jam’iyar PDP a Katsina kuma ɗaya daga cikin yaran Ministan Abuja Nyesom Wike aka baiwa kwangilar aikin hanyar tun farko, lamarin da bai yi masu daɗi ba, inda suka shiga suka fita aka dakatar da aikin, wanda yanzu ba a san matsayin da aikin hanyar yake ciki ba.

Yanzu dai abin jira a gani shi ne, ko shugaban ƙasa zai sake bada aikin hanyar a wani kamfanin da gwamna Dikko Raɗɗa da Hon. Ibrahim Kabir Masari suke so ko kuwa shikenan ruwa ta sha?

Tinubu
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina

MASU ALAKA

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

July 27, 2026
Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka
Labarai

Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

July 27, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Manyan Labarai

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Next Post
Wasu Matan Arewa Da Suka Yi Fice (2)

Wasu Matan Arewa Da Suka Yi Fice (2)

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

July 27, 2026
Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

July 27, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
Tinubu

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Tinubu

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.