ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Uwargida Za Ta Hada Miyar Uwaidu

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Miyar

Assalamu alaikum masu karatu, barkanmu da sake haduwa da ku a wannan makon cikin shirin namu mai farin jini da albarka na Girki Adon Mata.

A yau shafin na mu zai koya muku yadda uwargida za ta hada miyar Uwaidu:

Abubuwan da uwargida za ki tanada

ADVERTISEMENT

Nama, uwaidu, tattasai, tumatur, kayan yaji, daddawa, alayyahu, manja, magi, gishiri, kori, albasa.

Da farko uwargida za ki tafasa naman ki, na rago ne ko na shanu ko kuwa na kaza, idan kuma hada su za ki yi kamar na rago da na kaza duk za ki iya, sai ki zuba su a tukunya ki wanke su, sannan ki kawo gishiri da dan magi da kori da albasa ki zuba ki dora tafasarsa, idan ya yi daidai yadda kike bukata sai ki sauke shi ki zuba mai a tukunyar da za ki yi miyar.

LABARAI MASU NASABA

Amfanin Man Kwakwa Guda 11

Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada

Sannan sai ki kwashe ki soya shi, idan ya soyu sai ki kawo kayan miyarki tattasai da tumatur da taruhu idan kina so wanda dama kin jajjaga su ki zuba ki zuba yankakkiyar albasarki sannan ki kawo dakakkiyar daddawa ki zuba, ki dan soya su sama-sama sai ki kawo ruwan tafasar naman ki zuba, ki zuba magi, gishiri, kayan yaji, kori ki juya su, ki rufe kibar shi ya tafasa.

Daga nan sai ki kawo uwaido ki zuba wanda dama kin wanke shi, kin gyara shi kuma kin tafasa shi da ‘yar kanwa ki zuba shi, ki barshi ya dan dahu, sannan ki kawo alayyahu wanda shi kin gyara shi kin kuma yanka shi ki zuba ki dan bar shi ya dahu. Shi kenan kin kammala.

Gaskiya miyar ta hadu ga kyau ga dadi, kuma za ki iya ci da tuwon samo, sakwara da dai sauransu. A ci dadi lafiya

Miyar
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasihar Da Ya Dace Dukkan Iyaye Su Yi Wa ‘Yaƴansu Yayin  Aure?
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Ko Kin San… Cututtukan Da Man Ridi Ke Warkarwa?

MASU ALAKA

Amfanin Man Kwakwa Guda 12
Girke-Girke

Amfanin Man Kwakwa Guda 11

May 17, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Girke-Girke

Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada

May 10, 2026
Yadda Ake Hada Dafadikan Taliya (Jollof Spaghetti)
Girke-Girke

Yadda Ake Hada Dafadikan Taliya (Jollof Spaghetti)

April 25, 2026
Next Post
Rana Ta 3: Duk Da Dokar Hana Fita Masu Zanga-zanga Sun Fito A Kano

Rana Ta 3: Duk Da Dokar Hana Fita Masu Zanga-zanga Sun Fito A Kano

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.