ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, August 3, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Ƙura

by Sani Anwar and Sulaiman
10 months ago
Tinubu

A makon da ya gabata ne, Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ya yi afuwa ga wasu daga cikin fursunoni na wannan kasa.

 

Jerin sunayen wadanda aka yi wa afuwar, wanda mai bai wa shugaban kasa shawara kan yada labarai, Bayo Onanuga ya fitar, sun hada da mutanen da aka yanke wa hukunci, kan laifuffuka daban-daban da suka hada da:

ADVERTISEMENT
  • Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika
  • Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

Masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba, masu safarar miyagun kwayoyi, ‘yan kasashen waje, Manjo Janar Mamman Batsa, Manjo Akubo, Farfesa Magaji Garba da sauran wadanda suka aikata manyan laifuka, irin su Maryam Sanda, Ken Saro Wiwa Ogoni su takwas, na daga cikin mutane 175 da shugaban kasar ya yi wa afuwa.

 

LABARAI MASU NASABA

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

Kamar yadda rahotanni suka tabbatar, Shugaba Tinubu ya yi wa akasarinsu sassauci ne, bisa rahotannin da ke cewa; wadanda aka yanke wa hukuncin, sun nuna matukar nadama da kuma halin kirki. Haka zalika, ya yafe wa wasu saboda tsufa da samun sabbin fasahohin sana’o’i, ko shiga Jami’ar NOUN. Shugaba Tinubu ya kuma gyara rashin adalcin tarihi, wanda Turawan mulkin mallaka na Burtaniya suka yi wa Sir Herbert Macaulay, daya daga cikin masu kishin kasa a Nijeriya.

 

A takaice dai, kwamitin bai wa shugaban kasa shawara, kan jinkai, karkashin jagorancin babban mai shari’a; kuma ministan shari’a, Prince Lateef Olasunkanmi Fagbemi, ya bayar da shawarar yin afuwa ga fursunoni biyu da 15 da aka yankewa hukunci, wadanda 11 daga cikinsu sun rasu. Kazalika, kwamitin ya ba da shawarar yin afuwa ga fursunoni 82 tare da sassauta hukuncin dauri na fursunoni 65. Fursunonin bakwai da aka yanke wa hukuncin kisa, su ma sun shiga cikin jeren afuwar da shugaban kasar ya yi. Sannan, kwamitin ya ba da shawarar cewa; shugaban kasa ya mayar da hukuncin kisa zuwa daurin rai da rai.

 

Fagbemi ya gabatar da rahoton kwamitin a taron majalisar kasa, wanda shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya jagoranta.

 

A bangare guda kuma, ‘yan Nijeriya da dama na fadin albarkacin bakinsu, dangane da wannan afuwa da shugaban kasa ya yi wa masu laifukan daban-daban, wasu na da ra’ayin cewa; mafi yawan wadanda aka yi wa afuwar, ‘yan kwaya ne da rikakkun ‘yan ta’adda da kuma wadanda tuni suka mutu. A cikin masu nuna takaicin nasu; akwai tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ‘yan siyasa, masu sharhi kan al’amuran yau da kullum, jam’iyyun adawa da kuma iyalai da sauran abokanan arziki da al’amarin ya shafa.

 

Iyalan marigayi Bilyaminu Ahmed Bello, na daya daga cikin wadanda suka bayyana rashin jin dadinsu, kan afuwar da shugaban kasa ya yi wa Maryam Sanda, wadda aka yankewa hukuncin kisa bisa laifin kashe mijinta, wadanda suka bayyana yin afuwar a matsayin wani mummunan zalinci da aka tafka musu.

 

A wata sanarwa da aka fitar ranar Litinin da ta gabata dauke da sa hannun Dakta Bello Haliru Mohammed (Dangaladiman Gwandu), a madadin ‘yan’uwa, ‘yan’uwan marigayin sun bayyana matakin da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya dauka na yi wa Sanda afuwa a matsayin wani mummunan sake fama musu raunukan da suka samu da kuma rashin adalci ga dan’uwan nasu.

 

Iyalan Bilyaminun sun bayyana cewa, sun ji matukar takaicin sakin Maryam da aka yi, inda suka bayyana hakan; a matsayin wani yunkuri na dadada wa danginta tare da yin watsi da bacin ran da ya addabi ‘yan’uwa da sauran abokan arzikin marigayin.

 

Maryam, mai shekaru 37, na daya daga cikin mutum 175 da aka yanke wa hukunci, aka kuma yi wa afuwa da jin kai a ranar Alhamis da ta gabata, a karkashin ikon shugaban kasa.

 

A bangare guda kuma, kwatsam! Sai ga sanarwar mahaifin mijin Maryam Sandan cewa; shi da kansa ne ya roki Shugaban Kasa Tinubu, ya yi wa sirikar tasa afuwa.

 

A cewarsa, ya dade yana neman rokon a yi wa Maryam sassauci tare da afuwa, wacce ke fuskantar hukuncin kisa, tun bayan yanke mata hukuncin da aka yi.

 

Alhaji Ahmed Bello Isa, wanda ya bayyana hakan a wata tattaunawa ta hadin gwiwa da aka yi da shi a ranar Talatar da ta gabata a Abuja tare da Alhaji Garba Sanda, mahaifin Maryam, ya bayyana cewa; dalilinsa na yin hakan, saboda tausayi tare kuma son ganin an sako masa surukarsa, domin ta samu ta kula da ‘ya’yanta guda biyu, domin kuwa, kashe ta ba zai taba dawo masa da dansa ba.

 

Ya kara da cewa, “Na yafe wa Maryam da aka samu da laifin kisan dana, kafin a kammala shari’a, na yi iya kokarina na sanar da ‘yansanda da kotu cewa; ba na so a gurfanar da ita a gaban kuliya, domin kuwa jikoki kamar yadda suka rasa mahaifinsu, haka nan kuma za su rasa mahaifiya.

 

“Na dauki wannan a matsayin iftila’i, wanda Allah ya jarrabe ni da shi, a kan abin da ya faru da dana, sannan kuma ko kadan ban ga laifin Maryam ba, amma a lokacin da aka yanke mata hukuncin kisa, addu’a na yi mata tare da rokon Allah ya ji kan ta da rahama, sannan na ce; idan aka kashe ta, wa zai kula da ‘ya’yanta guda biyu? Kawai za su girma ne a matsayin marayu, babu soyayyar uba, babu ta uwa,” in ji shi.

 

Da aka tambaye shi game da maganar da ‘yan’uwa suka yi na nuna damuwarsu kan afuwar da shugaban kasa ya yi mata sai ya ce; “Kowa yana da ‘yancin fadin albarkacin bakinsa a cikin iyalansa, amma a matsayina na mahaifinsa, na yafe mata.

 

Shi ma da yake yin nasa jawabin, Alhaji Garba Sanda, mahaifin Maryam, ya nuna matukar godiyarsa ga Alhaji Bello da sauran daukacin iyalansa, bisa irin halin da suka tsinci kansu a ciki; wanda ba kasafai suke nunawa ba.

 

Iyalan biyu, sun bayyana cewa, sun zabi afuwa, tausayi da kuma imani fiye da ciwon da yake damun su, sannan kuma sun himmatu wajen hada kai; domin renon yaran biyu, cikin kwanciyar hankali da soyayya.

 

Shi ma a nasa bangaren, tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, ya zargi Shugaban Kasa Bola Tinubu, da yin amfani da ikon shugaban kasa na jin kai, ta hanyar yin afuwa ga mutum 175, yana mai cewa; matakin “ya gurgunta adalci”, sannan kuma yana da matukar hadari ga rashin bin doka da oda.

 

A cikin wata sanarwa da Atikun ya fitar, ta shafinsa na D a ranar Lahadin da ta gabata ya ce; hakkin yin afuwa, ba yana nufin rashin yin adalci ba ne ko tauye wa wani hakkinsa ba.

 

Har ila yau, Atiku ya soki shigar da mutanen da aka samu da aikata manyan laifuka, yana mai cewa; sakamakon wadanda aka yi wa afuwar, hakan na iya raunana imanin wasu daga cikin mutane tare da karfafawa wasu gwiwa, wajen ci gaba da aikata muggan laifuka.

 

Ya kara da cewa, bai kamata a bar yin afuwa ko jin kai ya hada su jera da aikata muggan laifuka da kuma rage aiwatar da adalci ba.

Tinubu
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Yadda Ciwon Hanta Ke Yaduwa Tsakanin Ma’aurauta
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
Tinubu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina
  • Sulaiman
    Iran Ta Musanta Iƙirarin Trump Kan Sabbin Tattaunawa da Amurka
  • Sulaiman
    ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara
  • Sulaiman
    Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

MASU ALAKA

DSS
Manyan Labarai

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

August 3, 2026
Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

August 3, 2026
Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026
Manyan Labarai

Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

August 3, 2026
Next Post
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai

Yadda 'Yan Bindiga Ke Zafafa Hare-hare A Jihohin Arewa Maso Yamma

LABARAI MASU NASABA

DSS

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

August 3, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Musanta Iƙirarin Trump Kan Sabbin Tattaunawa da Amurka

August 3, 2026
Zamfara

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara

August 3, 2026
Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

August 3, 2026
Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

August 3, 2026
Tinubu

WAFCON 2026: Ƴan Wasan Nijeriya 2 Ba Zasu Buga Wasan Ƙarshe Na Rukunin C Ba

August 2, 2026
Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

August 2, 2026
Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

August 2, 2026
Tinubu

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Ceto Mutane 9 A Zamfara

August 2, 2026
Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

August 2, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.