ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

 ‘Yan Adawa Sun Sauya Sabuwar Dabarun Kifar Da Tinubu A 2027

by Yusuf Shuaibu
5 months ago
Adawa

A daidai lokacin da zabe 2027 ke kara karatowa, ‘yan adawa sun sauya sabuwar dabaru na ganin sun kifar da gwamnatin Shugaban kasa, Bola Tinubu a zabe 2027.

Jam’iyyar PDP ta ce tana kara kokarin sake hada gidauniyar cikin gida da kafa hadin kan siyasa mai fadi a matsayin wani bangare na dabarunta na zaben 2027.

  • Rikicin Iran Da Amurka: Gabas Ta Tsakiya Ta Ɗauki Zafi
  • Dabara Ta Rage Ga Mai Shiga Rijiya

Mataimakin shugaban jam’iyyar na rikon kwarya a yakin kudu maso kudu, Emmanuel Ogidi, ya bayyana wannan a wata hira da kamfanin dillancin lamarai na Nijeriya (NAN), yana mai jaddada cewa jam’iyyar na ci gaba da dagewa wajen kare dimokuradiyya da sake tsara kanta a matsayin sahihin jam’iyyar adawa duk da rashin jituwa da ke ci gaba a wanzuwa a cikinta.

ADVERTISEMENT

Ogidi ya amince cewa PDP na fuskantar kananan matsaloli, amma ya jaddada cewa wadannan kalubale ba za su darkushe burinta na kare dimokiradiyya ba. Ya bayyana jam’iyyar a matsayin guda daya tilo mai ingancin adawa, kuma ya yi alkawarin cewa ba za ta ba ‘yan Nijeriya kunya ba.

A cewarsa, PDP tana sane da tsananin yanayin siyasar kasar a yanzu kuma tana da niyyar cika tsammanin ‘yan Nijeriya wadanda ke ganin jam’iyyar a matsayin tsarin dimokiradiyya.

LABARAI MASU NASABA

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

Ogidi ya ce babban abin da PDP za ta mayar da hankali a kai wajen zabukan 2027 shi ne, kare dimokuradiyya, bunkasa hadin kan kasa da kuma ba ‘yan Nijeriya wani zabin gaskiya ga jam’iyyar da ke mulki.

Ya zargi APC da ba da fifiko ga samun nasarorin zabe fiye da ingantaccen shugabanci, yana tambaya dalilin da ya sa jam’iyyar mai mulki, kasa da shekaru biyu tana kan kujerar mulki, amma ta fi mai da hankali kan yakin neman zabe fiye da magance kalubalen shugabanci.

Jigon jam’iyyar PDP ya yi gargadin cewa lalacewar cibiyoyin dimokuradiyya na iya jefa kasar cikin rashin daidaito, yana tabbatar da cewa jam’iyyar za ta yi duk mai yiwuwa don hana fadawa irin wannan yanayi.

Kazalika, jam’iyyar ADC, ta yi gargadi kan abin da ta bayyana a matsayin yunkurin da ake yayatawa kuma aka tsara shi domin tilasta wa ma’aikatan gwamnatin Nijeriya yin rajistar APC, ta hanyar aikin da ke gudana ta intanet da suke gudanarwa a halin yanzu.

A cikin wata sanarwa da sakataren yada labarai na kasa na jam’iyyar, Malam Bolaji Abdullahi, ya sanya hannu a kai, ta bayyana hakan.

ADC ta ce ta samu rahotanni daga sassa daban-daban na kasar wanda ke ikirarin cewa ana matsa wa ma’aikatan gwamnati su yi rajista a jam’iyyar gwamnati a matsayin sharadi don samun tsaro a aiki, ci gaban sana’a, ko kuma ci gaba da samun abin dogaro da shi.

Jam’iyyar ta bayyana wannan yunkuri a matsayin abin da ya sab awa tsarin dimokuradiyya, tana gargadin cewa tilasta wa ‘yan kasa su kasance mambobi a wata jam’iyyar siyasa yana daidai da manyan take hakkin Dan’adam da kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya ya tanada.

A cewar ADC, abin da APC ke kira rajistar intanet yana kara daukar sabon salo na tilasta wa mutane shiga cikin jam’iyya ba da yardarsu ba.

ADC ta kara yin gargadi cewa ana zargin wannan aiki na iya zama barazana ga kwararrun ma’aikatan gwamnatin Nijeriya, wanda suka ce a bisa ka’ida ana tsammanin ya kasance mai zaman kansa, bisa cancanta, kuma aminci ga jiha ba ga kowanne jam’iyyar siyasa ba.

ADC ta yi kira ga hukumomi ciki har da hukumar kariya ta bayanai ta Nijeriya (NDPC) da kungiyoyin ma’aikata da kungiyoyin fararen hula da na kasa da kasa, da su sa ido sosai kan lamarin, tana gargadin cewa hakan na iya zama cin zarafi na iko da kuma yiwuwar take hakkin Dan’adam.

Adawa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

MASU ALAKA

makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

June 26, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Next Post
Siffofin Manzon Allah S.A.W (II)

Mece Ce Soyayyar Annabi SAW?

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

July 9, 2026
Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

July 9, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A  Jihar Benuwai

’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A Jihar Benuwai

July 9, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.