ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

 ‘Yan Adawa Sun Sauya Sabuwar Dabarun Kifar Da Tinubu A 2027

by Yusuf Shuaibu
4 months ago
Adawa

A daidai lokacin da zabe 2027 ke kara karatowa, ‘yan adawa sun sauya sabuwar dabaru na ganin sun kifar da gwamnatin Shugaban kasa, Bola Tinubu a zabe 2027.

Jam’iyyar PDP ta ce tana kara kokarin sake hada gidauniyar cikin gida da kafa hadin kan siyasa mai fadi a matsayin wani bangare na dabarunta na zaben 2027.

  • Rikicin Iran Da Amurka: Gabas Ta Tsakiya Ta Ɗauki Zafi
  • Dabara Ta Rage Ga Mai Shiga Rijiya

Mataimakin shugaban jam’iyyar na rikon kwarya a yakin kudu maso kudu, Emmanuel Ogidi, ya bayyana wannan a wata hira da kamfanin dillancin lamarai na Nijeriya (NAN), yana mai jaddada cewa jam’iyyar na ci gaba da dagewa wajen kare dimokuradiyya da sake tsara kanta a matsayin sahihin jam’iyyar adawa duk da rashin jituwa da ke ci gaba a wanzuwa a cikinta.

ADVERTISEMENT

Ogidi ya amince cewa PDP na fuskantar kananan matsaloli, amma ya jaddada cewa wadannan kalubale ba za su darkushe burinta na kare dimokiradiyya ba. Ya bayyana jam’iyyar a matsayin guda daya tilo mai ingancin adawa, kuma ya yi alkawarin cewa ba za ta ba ‘yan Nijeriya kunya ba.

A cewarsa, PDP tana sane da tsananin yanayin siyasar kasar a yanzu kuma tana da niyyar cika tsammanin ‘yan Nijeriya wadanda ke ganin jam’iyyar a matsayin tsarin dimokiradiyya.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ogidi ya ce babban abin da PDP za ta mayar da hankali a kai wajen zabukan 2027 shi ne, kare dimokuradiyya, bunkasa hadin kan kasa da kuma ba ‘yan Nijeriya wani zabin gaskiya ga jam’iyyar da ke mulki.

Ya zargi APC da ba da fifiko ga samun nasarorin zabe fiye da ingantaccen shugabanci, yana tambaya dalilin da ya sa jam’iyyar mai mulki, kasa da shekaru biyu tana kan kujerar mulki, amma ta fi mai da hankali kan yakin neman zabe fiye da magance kalubalen shugabanci.

Jigon jam’iyyar PDP ya yi gargadin cewa lalacewar cibiyoyin dimokuradiyya na iya jefa kasar cikin rashin daidaito, yana tabbatar da cewa jam’iyyar za ta yi duk mai yiwuwa don hana fadawa irin wannan yanayi.

Kazalika, jam’iyyar ADC, ta yi gargadi kan abin da ta bayyana a matsayin yunkurin da ake yayatawa kuma aka tsara shi domin tilasta wa ma’aikatan gwamnatin Nijeriya yin rajistar APC, ta hanyar aikin da ke gudana ta intanet da suke gudanarwa a halin yanzu.

A cikin wata sanarwa da sakataren yada labarai na kasa na jam’iyyar, Malam Bolaji Abdullahi, ya sanya hannu a kai, ta bayyana hakan.

ADC ta ce ta samu rahotanni daga sassa daban-daban na kasar wanda ke ikirarin cewa ana matsa wa ma’aikatan gwamnati su yi rajista a jam’iyyar gwamnati a matsayin sharadi don samun tsaro a aiki, ci gaban sana’a, ko kuma ci gaba da samun abin dogaro da shi.

Jam’iyyar ta bayyana wannan yunkuri a matsayin abin da ya sab awa tsarin dimokuradiyya, tana gargadin cewa tilasta wa ‘yan kasa su kasance mambobi a wata jam’iyyar siyasa yana daidai da manyan take hakkin Dan’adam da kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya ya tanada.

A cewar ADC, abin da APC ke kira rajistar intanet yana kara daukar sabon salo na tilasta wa mutane shiga cikin jam’iyya ba da yardarsu ba.

ADC ta kara yin gargadi cewa ana zargin wannan aiki na iya zama barazana ga kwararrun ma’aikatan gwamnatin Nijeriya, wanda suka ce a bisa ka’ida ana tsammanin ya kasance mai zaman kansa, bisa cancanta, kuma aminci ga jiha ba ga kowanne jam’iyyar siyasa ba.

ADC ta yi kira ga hukumomi ciki har da hukumar kariya ta bayanai ta Nijeriya (NDPC) da kungiyoyin ma’aikata da kungiyoyin fararen hula da na kasa da kasa, da su sa ido sosai kan lamarin, tana gargadin cewa hakan na iya zama cin zarafi na iko da kuma yiwuwar take hakkin Dan’adam.

Adawa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

MASU ALAKA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
Next Post
Siffofin Manzon Allah S.A.W (II)

Mece Ce Soyayyar Annabi SAW?

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026
Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

June 14, 2026
An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

June 14, 2026
Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

June 14, 2026
Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin

Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.