ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe 14, Sun Yi Garkuwa Da 81 A Sokoto Da Katsina

by Sulaiman
4 years ago
kudancin kaduna

‘Yan bindiga sun hallaka mutane goma sha hudu (14) tare da yin garkuwa da wasu mutane har tamanin da daya (81) a jihohin Sokoto da Katsina.

 

A kudancin jihar Sokoto, mutum 14 aka kashe aka sace 73 ciki har da mata da yara kanana.

ADVERTISEMENT
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Hedikwatar ‘Yansanda Sun Saki Daurarru A Anambra

Hare-haren wadanda suka wakana a kauyuka daban-daban da suke karamar hukumar Sabon Birni, Gada da karamar hukumar Goronyo.

 

LABARAI MASU NASABA

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

Rahotonni sun zo kan cewa kusan a lokaci guda aka kai hare-haren a kuma wuraren daban-daban dukka a ranar Litinin din da ta gabata.

 

Da ya ke ganawa da Daily Trust, wani basarake a Sabon Birni wanda ya nemi a sakaye sunansa, ya shaida cewar yankuna uku ne da suke karamar hukumar aka kai harin inda aka kashe mutum 11 a cikinsu.

 

Ya ce kauyukan sun hada da Gatawa da Dangari da kuma Kurawa.

 

Shugaban ‘yan Bijilante a Sabon Birni Musa Muhammad da Dan majalisar da ke wakiltar mazabar Sabon Birni ta kudu a Majalisar Dokokin Jihar, Aminu Almustapha Boza, sun ce an kashe mutumin ne a gonarsa wajajen karfe 5 na yammacin ranar Litinin.

 

Boza ya ce an yi garkuwa da mutane da dama a wannan harin.

 

Shugaban karamar hukumar Goronyo, Abdulwahab Goronyo, ya nuna damuwarsa kan harin tare da cewa mutum biyu ne aka kashe a yankin nasa tare da garkuwa da wasu 23 a kauyukan Shinaka da Kagara a ranar Litinin.

 

Shi ma Dan majalisar da ke wakiltar mazabar Gada ta Gabas a Majalisar Dokokin Jihar, Kabiru Dauda ya shaida cewar mutum sama da 50 ciki har da mata da kananan yara ne aka sace a ranar Litinin.

 

Kazalika a wani harin da ya faru makamancin wannan, an kashe mutum daya da sace tawas a kauyukan da ke karamar hukumar Batsari a jihar Katsina a daren ranar Talata.

 

Wani mazaunin Batsari da ya roki a sakaye sunansa, ya shaida wa ‘yan jarida cewa ‘yan bindigan sun kashe Malam Tasi’u bayan da suka sace mishi dabbobi.

 

Wata majiya ma ta ce wasu ‘yan bindiga da yawansu ya kai 10 sun kai hari kauyen Shirgi da ke Batsari a safiyar ranar Labara inda suka yi ta harbe-harbe a sama tare da yin garkuwa da wani mutum Alhaji Shuaibu Shirgi.

 

Sannan ya ce an Kuma sace wasu mata da yara ciki har da yarirai biyu.

 

Har zuwa lokacin aiko da labarin ba a samu ji daga Kakakin ‘yan sandan jihar SP Gambo Isah ba.

'Yan Bindiga
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • Sulaiman
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • Sulaiman
    Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
  • Sulaiman
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

MASU ALAKA

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala
Labarai

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON
Labarai

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu
Labarai

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Next Post
PDP Ta Yi Barazanar Hukunta Gwamnonin G-5 Kan Hada Kai Da Tinubu

PDP Ta Yi Barazanar Hukunta Gwamnonin G-5 Kan Hada Kai Da Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.