ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe 14, Sun Yi Garkuwa Da 81 A Sokoto Da Katsina

by Sulaiman
3 years ago
kudancin kaduna

‘Yan bindiga sun hallaka mutane goma sha hudu (14) tare da yin garkuwa da wasu mutane har tamanin da daya (81) a jihohin Sokoto da Katsina.

 

A kudancin jihar Sokoto, mutum 14 aka kashe aka sace 73 ciki har da mata da yara kanana.

ADVERTISEMENT
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Hedikwatar ‘Yansanda Sun Saki Daurarru A Anambra

Hare-haren wadanda suka wakana a kauyuka daban-daban da suke karamar hukumar Sabon Birni, Gada da karamar hukumar Goronyo.

 

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Rahotonni sun zo kan cewa kusan a lokaci guda aka kai hare-haren a kuma wuraren daban-daban dukka a ranar Litinin din da ta gabata.

 

Da ya ke ganawa da Daily Trust, wani basarake a Sabon Birni wanda ya nemi a sakaye sunansa, ya shaida cewar yankuna uku ne da suke karamar hukumar aka kai harin inda aka kashe mutum 11 a cikinsu.

 

Ya ce kauyukan sun hada da Gatawa da Dangari da kuma Kurawa.

 

Shugaban ‘yan Bijilante a Sabon Birni Musa Muhammad da Dan majalisar da ke wakiltar mazabar Sabon Birni ta kudu a Majalisar Dokokin Jihar, Aminu Almustapha Boza, sun ce an kashe mutumin ne a gonarsa wajajen karfe 5 na yammacin ranar Litinin.

 

Boza ya ce an yi garkuwa da mutane da dama a wannan harin.

 

Shugaban karamar hukumar Goronyo, Abdulwahab Goronyo, ya nuna damuwarsa kan harin tare da cewa mutum biyu ne aka kashe a yankin nasa tare da garkuwa da wasu 23 a kauyukan Shinaka da Kagara a ranar Litinin.

 

Shi ma Dan majalisar da ke wakiltar mazabar Gada ta Gabas a Majalisar Dokokin Jihar, Kabiru Dauda ya shaida cewar mutum sama da 50 ciki har da mata da kananan yara ne aka sace a ranar Litinin.

 

Kazalika a wani harin da ya faru makamancin wannan, an kashe mutum daya da sace tawas a kauyukan da ke karamar hukumar Batsari a jihar Katsina a daren ranar Talata.

 

Wani mazaunin Batsari da ya roki a sakaye sunansa, ya shaida wa ‘yan jarida cewa ‘yan bindigan sun kashe Malam Tasi’u bayan da suka sace mishi dabbobi.

 

Wata majiya ma ta ce wasu ‘yan bindiga da yawansu ya kai 10 sun kai hari kauyen Shirgi da ke Batsari a safiyar ranar Labara inda suka yi ta harbe-harbe a sama tare da yin garkuwa da wani mutum Alhaji Shuaibu Shirgi.

 

Sannan ya ce an Kuma sace wasu mata da yara ciki har da yarirai biyu.

 

Har zuwa lokacin aiko da labarin ba a samu ji daga Kakakin ‘yan sandan jihar SP Gambo Isah ba.

'Yan Bindiga
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
PDP Ta Yi Barazanar Hukunta Gwamnonin G-5 Kan Hada Kai Da Tinubu

PDP Ta Yi Barazanar Hukunta Gwamnonin G-5 Kan Hada Kai Da Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.