ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe 14, Sun Yi Garkuwa Da 81 A Sokoto Da Katsina

by Sulaiman
3 years ago
kudancin kaduna

‘Yan bindiga sun hallaka mutane goma sha hudu (14) tare da yin garkuwa da wasu mutane har tamanin da daya (81) a jihohin Sokoto da Katsina.

 

A kudancin jihar Sokoto, mutum 14 aka kashe aka sace 73 ciki har da mata da yara kanana.

ADVERTISEMENT
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Hedikwatar ‘Yansanda Sun Saki Daurarru A Anambra

Hare-haren wadanda suka wakana a kauyuka daban-daban da suke karamar hukumar Sabon Birni, Gada da karamar hukumar Goronyo.

 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Rahotonni sun zo kan cewa kusan a lokaci guda aka kai hare-haren a kuma wuraren daban-daban dukka a ranar Litinin din da ta gabata.

 

Da ya ke ganawa da Daily Trust, wani basarake a Sabon Birni wanda ya nemi a sakaye sunansa, ya shaida cewar yankuna uku ne da suke karamar hukumar aka kai harin inda aka kashe mutum 11 a cikinsu.

 

Ya ce kauyukan sun hada da Gatawa da Dangari da kuma Kurawa.

 

Shugaban ‘yan Bijilante a Sabon Birni Musa Muhammad da Dan majalisar da ke wakiltar mazabar Sabon Birni ta kudu a Majalisar Dokokin Jihar, Aminu Almustapha Boza, sun ce an kashe mutumin ne a gonarsa wajajen karfe 5 na yammacin ranar Litinin.

 

Boza ya ce an yi garkuwa da mutane da dama a wannan harin.

 

Shugaban karamar hukumar Goronyo, Abdulwahab Goronyo, ya nuna damuwarsa kan harin tare da cewa mutum biyu ne aka kashe a yankin nasa tare da garkuwa da wasu 23 a kauyukan Shinaka da Kagara a ranar Litinin.

 

Shi ma Dan majalisar da ke wakiltar mazabar Gada ta Gabas a Majalisar Dokokin Jihar, Kabiru Dauda ya shaida cewar mutum sama da 50 ciki har da mata da kananan yara ne aka sace a ranar Litinin.

 

Kazalika a wani harin da ya faru makamancin wannan, an kashe mutum daya da sace tawas a kauyukan da ke karamar hukumar Batsari a jihar Katsina a daren ranar Talata.

 

Wani mazaunin Batsari da ya roki a sakaye sunansa, ya shaida wa ‘yan jarida cewa ‘yan bindigan sun kashe Malam Tasi’u bayan da suka sace mishi dabbobi.

 

Wata majiya ma ta ce wasu ‘yan bindiga da yawansu ya kai 10 sun kai hari kauyen Shirgi da ke Batsari a safiyar ranar Labara inda suka yi ta harbe-harbe a sama tare da yin garkuwa da wani mutum Alhaji Shuaibu Shirgi.

 

Sannan ya ce an Kuma sace wasu mata da yara ciki har da yarirai biyu.

 

Har zuwa lokacin aiko da labarin ba a samu ji daga Kakakin ‘yan sandan jihar SP Gambo Isah ba.

'Yan Bindiga
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Next Post
PDP Ta Yi Barazanar Hukunta Gwamnonin G-5 Kan Hada Kai Da Tinubu

PDP Ta Yi Barazanar Hukunta Gwamnonin G-5 Kan Hada Kai Da Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.