ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Na Ci Gaba Da Ganin Tasku Kan Tsadar Kayan Abinci

by Abubakar Abba
3 years ago
Abinci

A cikin ‘yan makwannin da suka gabata, ‘yan Nijeriya sun damu a cikin halin da suka tsinci kansu na ci gaba da fuskantar hauhawan farashin kayan abinci.

Hukumar kdiddiga ta kasa ta NBS ta bayyana cewa, hauhawan farashin kayan abinci daga shekara zuwa shekara, haka farashin man girki Burondi, hatsi, Tumatir, Doya, Kifi, Nama kayan lambu da sauransu, duk sun yi tashin gwaron Zabi.

  • Tsohon Wakilin LEADERSHIP Ya Zama Shugaban Gidan Rediyon Kano
  • Kiwon Lafiya: Yadda Dabi’un Ko-in-kula Ke Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke

Acewar hukumar ta NBS,  hauhawan farashin na kayan abinci, ya karu da kashi  22.22 a cikin dari a cikin watan Afirilun 2023.

ADVERTISEMENT

A bisa jin farashin kayan abinci da aka yi a wasu kasuwannin kasar nan,  a watan Yulin 2023, farashin ya nuna cewa, farashin Kwandon Tumatir daya, ya kai daga Naira   90,000 zuwa Naira 100,000, sabanin yadda a baya, ake sayar da Kwandon sa daya akan Naira 20,000.

Har ila yau, farashin Kwandon Tattasai wanda a baya ake sayar wa daga akan Naira 12,000 zuwa Naira 15,000,a yanzu ana sayar da Kwandon sa daya daga Naira   40,000 zuwa Naira 45,000.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Sauran kayan abincin kamar su, Taliyar Golden Penny Pasta ta Leda mai dauke da guda 20 duk katan daya ana sayar da shi kan Naira 10,200, haka Taliyar  Chicken Flabour Instant Noodles mai dauke da guda 40 a cikin Leda, ana sayar da duk katan daya kan Naira 8,000 samarin Knorr Chicken Maggi duk katan daya ana sayar da shi kan Naira 21,000.

Baya ga hauhawan farashin kayan abincin da ake ci gaba da fuskanta, an kuma danganta tashin gwaron Zabin kayan abincin akan tsadar farashin man fetur da rabar da shi da faduwar darajar Naira da kuma karancin kayan aikin gona.

Wadannan matsalolin da aka zayyano, kari da kalubalen rashin tsaro a kasar nan sun kara jefa, musamman talakawan kasar nan a cikin halin kuncin rayuwa.

A daya bangaren, wasu daga cikin manoman kasar nan, na ci gaba da fuskantar tsadar farashin kayan aikin noma, mussaman saboda tsadar farashin takin zamani da magungunan kashe kwari da rashin samun ingantaccen Irin noma da kuma rashin samar masu da kyayawan tsari, don yin noman rani.

Wani magidanci dan shekara 47 mai suna Emmanuel Ikechukwu da ke da zama a anguwar Orozo da ke Abuja wanda kuma yake da iyalai 6 ya bayyana cewa, wannan ne karo na farko a rayuwarsa da ya taba fuskantar matsin ruyuwa da ta hade masa da hauhawan farashin kayan abinci da tsadar sufuri.

A cewar Ikechukwu,“ Komai ya yi tsada a kasuwa har naji ba zan iya jurewa wa da hakan ba, ba a yi wani karin albashi ba amma farashin komai ya tashi. “

“Wannan ne karo na farko a rayuwarsa da ya taba fuskantar matsin ruyuwa da ta hade masa da hauhawan farashin kayan abinci da tsadar sufuri. “

Ya ce, me ya sa gwamnati ke kirkiro da tsare-tsaren da suke jefa rayuwar talakawan kasar nan a cikin halin kuncin rayuwar kuma shin, muna da sauran wata fata a Nijeriya kuwa  ?.

Wasu magidantan na ta hakilon samar wa iyalansu abinda za su ci, amma farashin kayan abincin, sai kara hauhawa yake yi.

Wasu gidajen da dama, sun rage yawan kayan abincin da  suke sayawa  ahalinsu, haka sun dakatar da sayen manya kayan more rayuwa da suka saba sayawa ahalansu.

Wani malamin makaranta mai suna Mallam Abubakar Usman wanda ke da zama a yankin Karu  a Abuja, shi ma kokawa ya yi akan hauhawan farashin kayan abincin.

Abubakar ya ce, a yanzu haka ni da dan uwa na, muna tsallake cin abinci har da ‘ya’yana uku saboda tashin gwaron Zabin na kayan masarufin.

Abinci
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Xi Jinping: Zurfafa Gyare-gyare A Cikin Jam’iyya Da Hukumomin Gwamnati, Muhimmin Mataki Ne Na Zamanintar Da Karfin Tafiyar Da Harkokin Mulki

Xi Jinping: Zurfafa Gyare-gyare A Cikin Jam'iyya Da Hukumomin Gwamnati, Muhimmin Mataki Ne Na Zamanintar Da Karfin Tafiyar Da Harkokin Mulki

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.