Gwamnatin Tarayya ta ayyana yankuna guda 2,000 a fadin jihohi 33 da kuma Babban Birnin Tarayya (FCT) a matsayin wuraren da ke fuskantar barazanar ambaliyar ruwa daban-daban. Cibiyar Ba da Gargadin Gaggawa kan Ambaliyar Ruwa ta Kasa (FEWSC) karkashin Ma’aikatar Muhalli ce ta fitar da wannan sabon hasashen a ranar Alhamis, 27 ga watan Agusta, wanda zai fara aiki daga 27 ga watan Agusta zuwa 9 ga watan Satumbar 2026. Daga cikin wannan adadi, an rarraba al’ummomi 915 a jihohi 19 a matsayin wadanda ke cikin matsanancin hadari da suke bukatar daukar matakin kariya na gaggawa.
Rahoton ya nuna cewa ambaliyar za ta iya afkuwa ne sakamakon danyar kasa, da tsananin ruwan sama, da kwararar ruwan sama kamarda bakin kwarya, da cikar magudanan ruwa, da kuma karuwar ruwan koguna. Dangane da rarraba wuraren, akwai wasu yankuna 429 a jihohi bakwai da ke fuskantar babban hadari, yayin da yankuna 656 a jihohi 13 suke cikin masu saukin hadari. Jihohin da ke cikin matsanancin hadarin sun hada da Kogi, da Binuwai, da Rivers, da Edo, da Delta, da Cross River, da Bayelsa, da Akwa Ibom, da Abia, da Anambra, da Ebonyi, da Enugu, da Imo, da Ekiti, da Legas, da Ogun, da Ondo, da Osun, da kuma Oyo.
A bangaren Arewacin kasar kuwa, cibiyar ta bayyana jihohin Binuwai, da Kogi, da Kwara, da Neja, da Adamawa, da Taraba, da Kebbi a matsayin masu fuskantar babban hadari, inda ta lissafa garuruwa kamar Ilorin, da Jebba, da Bida, da Minna, da Mokwa, da Yola, da Numan, da Jalingo, da Wukari, da Birnin da Kebbi. A gefe guda kuma, Abuja (FCT) na cikin jerin masu fuskantar hadari mai sauki, tare da jihohin Nasarawa, da Filato, da Bauchi, da Borno, da Gombe, da Yobe, da Zamfara, da Sakkwato, Katsina, da Kano, da Kaduna, da Jigawa. Wuraren da aka sanya wa ido a Abuja sun hada da Garki, da Wuse, da Maitama, da Asokoro, da Gwarinpa, da Kubwa, da Kuje, Gwagwalada, da Lugbe, da sauransu.
Daga karshe, cibiyar ta bukaci al’ummomin da ke cikin rukunin matsanancin hadari da su ci gaba da sanya ido, su tabbatar da hanyoyin ficewa don tsira, da kuma kare iyalai da muhimman kadarori. Ta bayar da tabbataccen kashedi ga mazauna yankunan da su guji zama, ko ajiye motoci, ko ajiye kayayyaki a wuraren da ambaliya ke bi, da dausayi, ko gabar koguna, da kuma magudanan ruwa da suka yi gangare.
An kuma umarci hukumomin ba da agajin gaggawa na jihohi, da jami’an muhalli, da masu sa ido a al’umma da su tsaurara lura a kewayen koguna, da rafuka, da gadoji, da madatsun ruwa, da kuma wuraren da zaizayar kasa ke shafa.














