ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Ta Dakatar Da Harajin Tsaron Intanet Kan Hada-hadar Kudade

by Sulaiman
2 years ago
Amurka

Gwamnatin Tarayya ta dakatar da harajin nan da aka ƙaƙaba wa masu ajiya a banki na tallafin tsaron yanar gizo.

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ne ya bayyana shigo da harajin kan kuɗaɗen da jama’a da kamfanoni ke turawa, wanda hakan ya haifar da ce-ce-ku-ce.

  • Umarnin CBN Na Cire Harajin Tsaron Intanet Ya Tayar Da Kura
  • Ba Za Ta Saɓu Ba, Mun Maka CBN A Kotu Kan Janye Wa Mutane Kuɗaɗensu A Asusunsu – Ƙungiyoyi

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana matakin da gwamnatin ta ɗauka a lokacin da yake zantawa da manema labarai bayan kammala taron Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC) a Fadar Gwamnati da ke Abuja ranar Talata.

ADVERTISEMENT

Ya ce ana yin nazari kan shirin. “Matsayin gwamnati shi ne an dakatar da wannan shirin. An ɗage shi. Matsayin gwamnati kenan a yanzu. Ana sake sabon nazari a kan sa.
“An maganar sosai a taron Majalisar (FEC) a jiya. Kun san cewa majalisar ta yau (taron) an ɗora ne kan na jiya,” inji ministan.

Ya ƙara da cewa: “Don haka, zan iya gaya maku cewa an dakatar da harajin tsaron yanar gizo. Gwamnati na sake tunani a kan sa.”

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

A ranar 6 ga watan Mayu ne Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya umarci bankuna, masu gudanar da hada-hadar kuɗi ta wayar salula, da masu ba da sabis na biyan kuɗi da su aiwatar da wannan harajin kamar yadda yake ƙunshe a cikin Dokar 2024 ta Laifin Yanar Gizo (Hanawa, Rigakafi, da sauran su) (gyara).

An tsara za a riƙa biyan harajin kashi 0.5 cikin ɗari kan duk kuɗin da mutum ya tura wa wani. Za a aika da kuɗaɗen ne zuwa Asusun Ajiyar Tsaron Yanar Gizo na Ƙasa wanda Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Tsaro (NSA) ke shugabanta.

Sai dai matakin ya fusata mutane matuƙa, lamarin da ya sa ake kira da a dakatar da shi.

A makon da ya gabata ma Majalisar Wakilai ta buƙaci CBN da ya janye umarnin da ya ba bankuna da su fara aiwatar da harajin, inda ta bayyana hakan a matsayin “shubuha”.

Wannan matakin na gwamnati ya kasance a matsayin martani ga wani ƙudiri kan buƙatar gaggawa na dakatarwa da kuma gyara aiwatar da harajin tsaron yanar gizo da ɗan majalisa Kingsley Chinda ya gabatar.

Gwamnati
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
  • Sulaiman
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • Sulaiman
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
  • Sulaiman
    Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Beijing Na Gaggauta Matakan Amfani Da Motoci Masu Aiki Da Wutar Lantarki Da Aka Samar Ta Makamashi Mai Tsabta

Beijing Na Gaggauta Matakan Amfani Da Motoci Masu Aiki Da Wutar Lantarki Da Aka Samar Ta Makamashi Mai Tsabta

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.