Aƙalla manoma guda 18 ne aka tabbatar da mutuwarsu, yayin da wasu da dama suka sami raunuka daban-daban sakamakon wani sabon hari da wasu ‘yan bindiga suka kai a jihar Filato.
Lamarin ya auku ne da yammacin jiya a lokacin da manoman ke tsaka da ayyuka a gonakansu, lamarin da ya jefa ɗaukacin yankin cikin fargaba da jimami.
Mazauna yankin sun bayyana cewa maharan sun farmaki gonakin ne ba zato ba tsammani, inda suka riƙa harbe-harbe ba ƙauƙautawa a kan duk wanda suka gani. Baya ga waɗanda aka kashe da waɗanda aka raunata, maharan sun kuma ƙona wasu kayayyakin amfanin gona da gidajen mazauna yankin gabanin isar jami’an tsaro.
Rundunar ƴansandan jihar ta tabbatar da faruwar wannan ɗanyen aiki, inda ta bayyana cewa tuni aka tura ƙarin jami’an tsaro na haɗin gwuiwa zuwa yankin domin kwantar da tarzoma da kuma hana aukuwar daukar fansa. Haka kuma, an kwashe waɗanda suka jikkata zuwa babban asibiti mafi kusa domin ba su kulawar gaggawa.
Shugabannin al’umma da ƙungiyoyin manoma na jihar sun yi kira ga gwamnatin tarayya da ta ɗauki ƙwararan matakai na din-din domin kare rayukan dubban manoma a jihar, musamman a wannan lokaci na damina. Shugabannin sun yi gargaɗin cewa idan ba a daƙile waɗannan hare-hare ba, hakan zai iya haifar da babbar barazana ga tsaron abinci a faɗin ƙasar.














Discussion about this post