CAF za ta gudanar da jadawalin wasannin neman gurbin shiga gasar cin kofin nahiyar Afirka ta 2027 ranar Talata a birnin Cairo, domin fara shirye-shiryen gasar da ƙasashen Kenya, Tanzania da Uganda za su karɓi baƙunci tare.
A cikin wata sanarwa da CAF ta fitar ranar Lahadi, ta bayyana cewa ƙasashe 48 za su gano rukunin da za su fafata a ciki yayin taron da za a gudanar a shalƙwatar Hukumar Kwallon Ƙafa ta Masar da ke Alkahira.
Gasar mai suna “AFCON PAMOJA 2027” inda kalmar “Pamoja” ke nufin “tare” a harshen Swahili ita ce karo na farko da ƙasashe uku za su haɗa kai wajen karɓar baƙuncin gasar. Za a gudanar da gasar daga ranar 19 ga Yuni zuwa 17 ga Yulin 2027, kuma hakan zai zama karo na farko da Gabashin Afirka zai karɓi baƙuncin AFCON tun bayan da Ethiopia ta shirya gasar a 1976.
Za a raba ƙasashen 48 zuwa rukuni 12 masu ƙungiyoyi huɗu-huɗu, inda ƙungiyoyi biyu na farko daga kowanne rukuni za su kai ga babbar gasar.
Sai dai saboda ƙasashen Kenya, Tanzania da Uganda sun riga sun samu tikitin shiga a matsayin masu masaukin baƙi, ƙungiya ɗaya kacal ce za ta samu damar tsallakewa daga rukuninsu.
Manyan ƙasashe irin su Senegal, da Morocco, da Egypt, da Algeria, da Nigeria, da Cameroon, da Côte d’Ivoire da South Africa na daga cikin ƙasashen da ake ganin za su yi fice, duk da cewa CAF ta ce ƙananan ƙasashe irin su Comoros da Gambia na ci gaba da rage tazarar da ke tsakaninsu da manyan ƙasashen nahiyar.















Discussion about this post