Hukumar Hisbah ta kammala shirye-shiryen fara aiwatar da dokar hana mata zama a gefen direban adaidaita sahu a Jihar Kano, da nufin ƙarfafa tarbiyya da kyawawan ɗabi’u a al’umma.
Daraktan Wayar da Kai na hukumar, Auwalu Ado Sheshe, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a, inda ya ce za a gudanar da aikin tare da haɗin gwiwar ƙungiyoyin direbobi da masu adaidaita sahu domin tsaftace harkar sufuri da daƙile abin da ya kira saɓawa koyarwar addini.
- Ganduje Ya Dakatar Da Shirin Kafa Hukumar Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano
- Hukumar Hisbah Ta Kano Ta Karɓi Ƙorafe-Ƙorafe Sama Da 12,000 A Shekarar 2025
Ya ce aikin zai maida hankali ne kan hana mata zama kusa da direbobin da ba muharramansu ba yayin hawa adaidaita sahu, tare da gargaɗin cewa duk wanda ya saɓa zai fuskanci hukunci.
Hukumar ta buƙaci direbobi da fasinjoji mata su bi umarnin, tana mai jaddada aniyarta na tabbatar da al’umma mai ɗabi’a ta gari bisa koyarwar Musulunci.















Discussion about this post