Shugaba Bola Tinubu ya ba da umarnin gudanar da cikakken binciken kwakwaf (forensic audit) kan tsarin biyan albashi na Integrated Personnel and Payroll Information System (IPPIS) da kuma dukkan hukumomin gwamnatin tarayya, sakamakon damuwa kan batun “ma’aikatan bogi,” da almundahanar biyan albashi da sauran gazawa a tsarin sa ido. Shugaban ya umarci Ministan Kudi kuma Taiwo Oyedele, da ya jagoranci aikin.
A cewar sanarwar da mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga ya fitar, wannan matakin ya biyo bayan ƙudurin Majalisar Zartarwa ta ƙasa (Federal Executive Council) na ranar 19 ga watan Agusta, 2026, dangane da sakamakon binciken da Hukumar ICPC ta gudanar kan “hukumomin bogi,” ma’aikatan bogi da sauran matsalolin sa ido a gwamnati.
Ana sa ran binciken zai tantance yanayi da girman gazawar da ke cikin tsarin sa ido na gwamnati, tare da gano yadda aka yi amfani da waɗannan giɓin. Ɓangaren farko na aikin zai mayar da hankali kan bincike a kan tsarin gwamnati, musamman IPPIS da sauran dandamalin biyan albashi, da ma’aikata, da fansho da kuɗi masu alaƙa da shi.
A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, aikin zai duba shari’o’in ma’aikatan bogi da almundahanar albashi da aka bayar da rahoto a kai, tare da daidaita adadin da ICPC ta gano, da bin diddigin yadda aka shigar da mutane bogi ko waɗanda ba su cancanta a jerin ma’aikata ba, tare da duba tsarin shigarwa, da tantance mutum, da kuma bayanan asusun banki.
Binciken zai kuma duba alaƙar da ke tsakanin IPPIS da sauran dandamalin gwamnati, ciki har da Government Integrated Financial Management Information System (GIFMIS), da Remita, da tsarin asusun bai ɗaya (Treasury Single Account) da Sub-Treasury Single Account.
Ana sa ran binciken zai tantance ko almundahanar da aka gano ta samo asali ne daga matsalolin tsarin, ko gazawar aiki, rashin rabon ayyuka yadda ya kamata, ko kuma sanadin kaucewa dokoki da gangan.














