ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago

Mun wallafa 30 ga Yuni, 2023

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Bago

A kwanan baya, Gwamnan Jihar Neja, Umar Bago ya kai ziyara ta musamman ga Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu a fadarsa da ke Abuja. Jim kadan bayan ganawarsu, wakilinmu na fadar shugaban kasa, JONATHAN INDA-ISAIAH ya tattauna da shi a kan makasudin ziyarar da kuma wasu abubuwa da suka shafi sha’anin tsaro a Jihar Neja. RABI’U ALI INDABAWA ya rubuta mana tattaunawar kamar haka:

Mene ne takamaimai ya kawo ka fadar shugaban kasa a wannan lokacin?

Na farko dai na zo na taya murna gaba ki daya, kuma mu kara jaddada masa cewa in Allah ya yarda gwamnoni musamman jam’iyyar APC za mu yi aiki da shi, kuma majalisa inda na fito kafin na zama gwamna, mun je mun kaddamar da zabe mun gaya musu baya kuma Allah ya sa abin da aka nema an samu. Amma bayan haka na zo ne da abu guda biyu, na farko mu Arewa ta Tsakiya muna kara kira da babbar murya cewa muna neman alfarma ga mai girma shugaban kasa a kara duba mu da idon rahma, bayan haka Ibtila’i na rashin tsaro da ya yi mana kakaka mun zo domin mu nemi taimako daga wurin gwamnatin tarayya don a samu waraka a wannan harka.

ADVERTISEMENT

An ganka kana rushe-rushe na wasu Hukumomi da aka ba da wa’adi me hakan yake nufi da wace kafa kenan ka fara da ita a Jihar Neja?

Na farko dai gwamnatinmu ba za mu yarda da zalunci ba, saboda haka mutane ba za su yi gini a kan hanyar ruwa ba ko hanyar wuta, wannan ba za mu yarda ba. Ko ofishin ‘yansanda da muka rusa mun rusa ne saboda yana kan hanyar ruwa. A baya idan an kunna ruwa sai ‘yansanda su hana kamfanin ruwa bude ruwa, kuma talaka yana son ruwa. Da muka samu wannan labarin muka fara da shi, wadansu kuwa karfa-karfa a baya sun zo sun gina gidajen mai a tsakanin mutane ba su da mu da cewa zai damu mutane ba, saboda haka suma din mun rufe su kuma mun kwace takardunsu kuma za mu rusa su gabaki daya, kuma wadannan filayen da muka karbe filaye ne na gwamnati, kuma asalin tsari na yadda za a tafiyar da jihar Neja, wannan wuraren shugabannin da suka gabata su kebe su ne saboda al’umma, saboda haka mutane sun zo suna so su handama ko sun karbe don suna dama, to shi ne Allah ya bamu dama mu juya alkiblar.

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

Fatan da ‘yan Jihar Neja ke da shi ita ce matsalar tsaro da yake addabarsu ko menene kake da shi ganin cewa hakan ya zo karshe?

To a cikin shirye-shiryen da muke da shi, na farko Jihar Neja tana daga cikin jihar da ta fi kowacce girma a fili, to yawancin dajikanmu ba a noma a ciki, to muna kira ga gwamnatin tarayya ta hada hannu da mu mu nome wadannan dazuka, na farko kenan. Na biyu kuma kafin a kai ga wurin muna neman taimakon ‘yan sanda da sojoji su zo su higa wadannan dazukan su zo su taya mu aiki don mu samu zama lafiya.

Bago
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Bago
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
Bago
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Wakilan Da Suka Halarci Taron Tunawa Da Cika Shekaru 60 Da Kasar Sin Ta Fara Tura Ma’aikatan Agajin Jinya Ga Kasashen Waje

Xi Jinping Ya Gana Da Wakilan Da Suka Halarci Taron Tunawa Da Cika Shekaru 60 Da Kasar Sin Ta Fara Tura Ma’aikatan Agajin Jinya Ga Kasashen Waje

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.