Kyaftin din Liverpool Virgil van Dijk ya ce Mohamed Salah zai samu bikin Girmamawa daga kungiyar duk da cewar babu tabbacin cewa zai buga wasan karshe na kungiyar a kakar wasa ta bana sakamakon raunin da ya samu, an tilasta wa dan wasan gaban na kasar Masar barin filin wasa sakamakon raunin da ya samu a cinyarsa a wasan da suka yi da Crystal Palace ranar Asabar.
Wasanni hudu kacal suka rage a kakar wasa ta bana, hakan yasa Liverpool ke fatan ya murmure kafin wasan karshe domin ya samu damar bugawa kungiyar kwallo a wasansa na karshe a kungiyar, dan wasan mai shekaru 33 zai bar kungiyar ta Liverpool bayan shafe shekaru 9 tareda lashe manyan kofuna ciki har da gasar Zakarun Turai da kuma Premier League na kasar Ingila.
Liverpool na jiran sakamakon gwajin da za a yi domin tantance girman raunin da Salah ya ji, kuma duk da cewa zai zama abin takaici ga Salah idan bai sami damar yin bankwana a filin wasa na Anfield ba, kyaftin din Liverpool Van Dijk ya ce hakan ba zai rage kimar dan wasan a idon yan Wasa da magoya bayan kungiyar ba, “Na san yana yin duk abin da zai iya don ya dawo filin wasa da wuri-wuri,” in ji Van Dijk, ” Amma ya sani cewa koda bai buga wasan karshen ba hakan ba zai rage komai a cikin kaunar da kungiyar da magoya bayanta ke nuna mashi ba, ya kara da cewa.















Discussion about this post