ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zazzabin Lassa: NCDC Ta Ce Mutum 411 Sun Kamu, 72 Sun Mutu A Cikin Mako 6 A Jihohi 21

by Muhammad
2 years ago
Lassa

Cibiyar Kula da Cututtuka ta Nijeriya (NCDC) ta ce ta yi rajistar mutane 411 da aka tabbatar sun kamu da cutar sannan 72 sun mutu sakamakon zazzabin Lassa a fadin jihohi 21 na tarayyar kasar daga mako daya zuwa mako shida na shekarar 2024.

Hukumar NCDC ta bayyana hakan ne a shafinta na yanar gizo ranar Alhamis.

  • Zazzabin Lassa Ya Yi Ajalin Mutum 154 A Nijeriya —NCDC
  • Diphtheria: Mutane 123 Sun Kamu, 38 Sun Mutu A Jihohi 4 – NCDC

Hukumar ta bayyana cewa adadin sabbin wadanda aka tabbatar sun karu daga 70 a cikin mako biyar zuwa 83 a cikin mako shida, tare da samun mutuwar mutane tara a cikin mako shida, wanda ya kai 5 ga Fabrairu zuwa Fed. 11.

ADVERTISEMENT

A cewar NCDC, kashi 65 cikin 100 na wadanda aka tabbatar sun fito ne daga jihohin Ondo da Edo da Bauchi, yayin da kashi 35 cikin 100 aka samu rahoto daga jihohi 17.

Hukumar ta ce adadin wadanda ake zargin sun kamu a shekarar 2024 (2,122) ya ragu idan aka kwatanta da adadin da aka bayar a daidai wannan lokacin a shekarar 2023 (8,280).

LABARAI MASU NASABA

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Ya ce mafi yawan shekarun da zazzabin Lassa ya shafa sun kai shekaru 21 zuwa 30, kuma sababbin ma’aikatan lafiya biyu sun kamu da cutar a cikin makon da ya gabata.

Hukumar NCDC ta ce, an fito d tsarin kula da masu fama da cutar zazzabin Lassa na kasa, da tsarin kula da al’amuran da suka shafi bangarori daban-daban don daidaita a dukkan matakai a Cibiyar Ayyukan Gaggawa (EOC).

Hukumar ta kuma zayyana wasu daga cikin kalubalen da take fuskanta a yakin da take da zazzabin Lassa a fadin kasar nan, wadanda suka hada da gabatar da cutar a makare da kuma rashin kyawun yanayin neman lafiya sakamakon tsadar magani da kula da lafiya.

Sauran ƙalubalen, in ji shi, sun haɗa da rashin tsabtar muhalli da kuma rashin fahimtar da ake gani a cikin al’ummomi masu dauke da ita.

Lassa
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
  • Muhammad
    ‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye

MASU ALAKA

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON
Labarai

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu
Labarai

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau
Rahotonni

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Next Post
Jami’an Kwastam Sun Kama Manyan Motoci 15 Maƙare Da Kayan Abinci A Sokoto

Hukumar Kwastom Ta Fara Sayarwa 'Yan Nijeriya Kayan Abincin Da Ta Kwace A Legas

LABARAI MASU NASABA

Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.