ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙudirin Ƙirƙiro Sabbin Jahohi 31 Ya Jawo Cece-kuce A Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
sabbin

Tun daga ranar Alhamis, 6 ga watan Fabrairu, lokacin da majalisar wakilai ta bayyana karbar shawarwarin kudirin samar da sabbin jihohi 31 a Nijeriya a wani yunkuri na ci gaba da sake fasalin kundin tsarin mulkin kasar na 1999, ya raba kan ‘yan Nijeriya a halin yanzu.

kudirin samar da sabbin jihohin idan aka samar da su, za su kara yawan jihohin Nijeriya daga 36 zuwa 67. A halin yanzu, Nijeriya na da jihohi 36, yankin kudu maso gabas na da jihohi biyar. Kudu maso yamma da kudu maso kudu da arewa ta tsakiya da arewa maso gabas suna da jihohi shida kowacce, yayin da arewa maso yamma ke da jihohi bakwai.

  • Ɗalibin Jami’a Ya Hallaka Kansa Saboda Matsin Rayuwa A Jihar Kwara
  • Wani Jami’in Ɗansanda Ya Bindige Kansa Har Lahira A Jihar Nasarawa

A cewar kudirin, yankin arewa ta tsakiya ta samu bukatu na samar da jihohi bakwai da suka hada da jihohin Benue Ala, Apa Agba, da Apa daga Jihar Benuwai ta yanzu; Jihohin Okun, Okura da Confluence daga Jihar Kogi ta yanzu, da kuma daukaka babban birnin tarayya Abuja zuwa matsayin jiha.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, a yankin arewa maso gabas, akwai shawarwarin samar da jihohin Amana, Katagum Sabannah da Muri daga jihohin Adamawa, Bauchi, Borno da Taraba na yanzu, bi da bi. Haka nan, akwai shawarwarin samar da sabbin jihohi biyar, wato New Kaduna da Gurrara, daga Jihar Kaduna ta yanzu; Jihohin Tiga da Ghari, daga Jihar Kano ta yanzu da kuma Kainji daga Jihar Kebbi.

A kudu maso gabas, jihohin da ake son kirkira sun hada da Etiti da za a samar daga jihohi biyar da ake da su a shiyyar; Adada daga Jihar Inugu, Orashi, Orlu da Aba da za a kirkiro daga jihohin Imo da Abiya.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Sannan a kudu maso kudu, masu goyon bayan sabbin jihohi suna son a samar da jihohin Ogoja, Warri, da Bori daga jihohin Kuros Ribas, Delta da Ribas, da kuma Jihar Obolo daga jihohin Ribers da Akwa Ibom na yanzu.

Daga kudu maso yamma kuwa, akwai shawarwarin samar da sabbin jihohi shida. Jihohin da ake shirin kirkira sun hada da Toru-ebe da za a sassaka daga jihohin Delta da Edo da Ondo na yanzu, da kuma jihohin Ibadan da Lagoon da za a sassaka daga jihohin Oyo da Legas, bi da bi. Sauran sun hada da Jihar Ijebu da za a samar daga Jihar Ogun ta yanzu da kuma jihohin Oke-Ogun da Ife-Ijesha da za a kirkiro daga jihohin Ogu da Oyo da Osun na yanzu.

Kwamitin majalisar kan sake fasalin kundin tsarin mulkin kasar nan, a wata sanarwa da ya aike wa mambobin majalisar wakilai, mai dauke da sa hannun mataimakin shugaban majalisar wakilai, Benjamin Kalu, wanda kuma shi ne shugaban kwamitin, ya umurci masu goyon bayan kirkiro sabbin jihohin da su sake gabatar da bukatarsu kamar yadda sashe na 8 (1) na kundin tsarin mulkin 1999 ya tanada.

“Kwamitin ya duba shawarwarin samar da sabbin jihohi kamar yadda sashe na 8(1) na kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya na shekarar 1999 ya tanada. Wannan sashe ya zayyana takamaiman bukatu wadanda dole ne a cika su don fara aikin kirkirar sabbin jihohi. Za a sake gabatar da shawarwari bisa la’akari da wadannan sharudda,” in ji Kalu.

Wasu ‘yan Nijeriya dai sun soki matakin, suna masu cewa abin da ya kamata shugabanni su mayar da hankali a kai shi ne, yadda za a mayar da kasar mulkin yanki ba wai samar da karin jihohi ba.

Masu yada wannan labari na ganin cewa Nijeriya ta fi samun shugabanci nagari a lokacin da ake tsarin milkin yankuna, lura da cewa samar da jihohi 12 daga yankuna hudu da gwamnatin mulkin soja ta Janar Yakubu Gowon ta yi ba don wani ci gaba ba ne, sai dai wani yunkuri ne na raunana yankin gabas a lokacin yakin Biafara.

Amma, akwai wadanda kuma suka yi jayayya cewa samar da jihohi yana kawo ci gaba ga mutanen da ke ganin an ware su kuma za su yi maraba da shawarwarin muddin sun bi ka’idojin kamar yadda ‘yan majalisar suka sake nanata a baya.

Haka kuma, akwai wasu da ba su yarda da samar da karin jihohi a Nijeriya gaba daya ba, amma suna da ra’ayin cewa a yi adalci a kara wa yankin kudu maso gabas karin jiha daya domin daidaita yankin da takwarorinsa.

kungiyoyin yankin biyu da suka yi kaurin suna wajen nuna adawa da matakin sun hada da kungiyar kabilar Yarbawa ta Afenifere da kuma kungiyar tuntuba ta Arewa (ACF). Dukkan bangarorin biyu sun bayyana shirin samar da jihar a matsayin abin dariya kuma ba amshesshe ba ne.

Sai dai kungiyar ta Afenifere ta bukaci majalisar dokokin kasar da ta mayar da hankali kan sauye-sauyen kundin tsarin mulkin kasar da zai raba madafun iko, da maido da albarkatun kasa a yankunan, da kuma bai wa jihohi ‘yancin cin gashin kansu domin su bunkasa cikin hanzari.

Haka zalika, kungiyar tuntuba ta Arewa, ta kuma bayyana rashin amincewarta da shirin samar da sabbin jihohi 31, inda ta bayyana ra’ayin a matsayin wanda bai kamata ba.

Amma, babbar kungiyar kare al’adun Igbo, Ohanaeze Ndigbo ta bi wata hanya ta daban. Tana da ra’ayin cewa a kara wa yankin kudu maso gabas sabbin jihohi domin magance kura-kuran da aka yi wa yankin dangane da batun samar da jihohi.

A nasa bangaren, Babban Lauyan Nijeriya kuma Farfesa a fannin shari’a, Cif Mike Ozekhome, ya bayyana hakan a matsayin almubazzaranci.

Shima da yake magana game da damuwar da ‘yan Nijeriya da dama ke da shi dangane da yadda ake tada zaune tsaye na samar da sabbin jihohi, Mista Osita Okechukwu, tsohon Darakta Janar na Muryar Nijeriya ya yaba da matakin a matsayin kyakkyawan misali ga hadin kan kasa.

Najeeb Bello ya kasa boye bacin ransa game da lmarin, inda ya ce, “Me zai hana smar da jihohi 311? A bari kowace karamar hukuma a Nijeriya ta zama jiha kawai.”

Bashir Ahmad yana goyan bayan samar da sabbin jihohi, amma ya bayar da shawara a kara karkasa Jihar Kano duba da yawan al’ummar da take da shi.

sabbin
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
2027: Ganawar Kwankwaso Da Aregbesola Ta Haifar Da Cece-kuce A Fagen Siyasar Nijeriya

2027: Ganawar Kwankwaso Da Aregbesola Ta Haifar Da Cece-kuce A Fagen Siyasar Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.