ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙwace Mulki A Hannun Tinubu Ne Kaɗai Hanyar Ceto Nijeriya A 2027 — ADC

by Leadership Hausa
8 months ago
Tinubu

Jam’iyyar haɗaka ta ADC ta bayyana cewa ƙwace mulki a hannun Shugaba ƙasa Bola Tinubu ne kaɗai hanyar ceto Nijeriya daga abin da ta bayyana a matsayin mummunan rikicin shugabancin ba a tava ganin irinsa ba.

Mai magana da yawun jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya bayyana hakan a ranar Juma’a a yayin wata hira a shirin siyasa na gidan talaijin na Channels, inda ya musanta cewa ba za a iya ceto ƙasar nan ba idan har wannan gwamnati tana kan mulki.

“Wannan shi ne a ajendar, amma ba shi ne ra’ayoyin ƴan Nijeriya gaba ɗaya ba. Sai da kuma babu yadda za a yi Tinubu na kan mulki a iya ceto Nijeriya.

ADVERTISEMENT

“A duk lokacin da mutane ke cewa za ka iya ɗaukewa da gudu da wani muhimmin abu ba tare da la’akari da yin tunani ba, tabbas wannan kalamun ƴan bindiga ne,” in ji Abdullahi.  

  • Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
  • Atiku Ya Yi Murna, Ya Yi Marhaba Da Peter Obi A ADC

Haka kuma Abdullahi ya nuna damuwarsa game da zargin da ake yi wa ƴan majalisa na sauya dokar haraji wanda aka ƙaƙaba wa ƴan Nijeriya a wannan shekara, ya sava wa dimokuraɗyyar ƙasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ya zargi gwamnati da aiwatar da wasu ƙudirorin na ƙasashen ƙetare waɗanda ba su dace da tsarin mulkin ƙasar nan ba.

“Gwamnatin da za ta iya amicewa da dokar da aka yi wa cushe, me kake kiran irin wannan gwamnati?” ya tambaya.

Ya musanta cewa a cikin kasafin kuɗin 2026, yawan kuɗaɗen da za a kashe a wasu abubuwa marasa fifiko ya nuna cewa gwamnatin ta gaza. Ya ce saka irin wannan adadin a vangaren tsaro na cikin gida zai ba da sakamako mafi kyau fiye da ƙoƙarin tabbatar wa shugabannin ƙasashen waje cewa Nijeriya tana zaune lafiya.

“Ba su damu da yadda ‘yan Nijeriya ke ci gaba da mutuwa. Ba su damu cewa mutane na ci gaba da hallaka ba. Abin da suke so kawai shi ne, su sami fada a gaban Amurkawa,” in ji Abdullahi.

Mai magana da yawun ADC ya nuna damuwa kan yarjejeniyar fahimtar juna ta likitanci tsakanin Nijeriya da Amurka, wadda aka ruwaito an sanya hannu a kanta a ranar 19 ga Disamba, wanda ya yi iƙirarin cewa za ta bai wa Amurka ikon sarrafawa da rarraba kuɗaɗe sosai duk da cewa Nijeriya ce ke bayar da mafi girman gudummawar kuɗi.

“Babu ɗan Nijeriya da ya ga cikakkun bayanan wannan yarjejeiya” in ji shi, yana bayyana sharuɗɗan a matsayin abin mamaki yayin da ya yi tambayoyi game da ikon mallaka na ƙasa da ƙasa.

Tinubu
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Osimhen Ya Zura Ƙwallonsa Ta 50 A Galatasaray

Osimhen Ya Zura Ƙwallonsa Ta 50 A Galatasaray

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.