ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙwace Mulki A Hannun Tinubu Ne Kaɗai Hanyar Ceto Nijeriya A 2027 — ADC

by Leadership Hausa
5 months ago
Tinubu

Jam’iyyar haɗaka ta ADC ta bayyana cewa ƙwace mulki a hannun Shugaba ƙasa Bola Tinubu ne kaɗai hanyar ceto Nijeriya daga abin da ta bayyana a matsayin mummunan rikicin shugabancin ba a tava ganin irinsa ba.

Mai magana da yawun jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya bayyana hakan a ranar Juma’a a yayin wata hira a shirin siyasa na gidan talaijin na Channels, inda ya musanta cewa ba za a iya ceto ƙasar nan ba idan har wannan gwamnati tana kan mulki.

“Wannan shi ne a ajendar, amma ba shi ne ra’ayoyin ƴan Nijeriya gaba ɗaya ba. Sai da kuma babu yadda za a yi Tinubu na kan mulki a iya ceto Nijeriya.

ADVERTISEMENT

“A duk lokacin da mutane ke cewa za ka iya ɗaukewa da gudu da wani muhimmin abu ba tare da la’akari da yin tunani ba, tabbas wannan kalamun ƴan bindiga ne,” in ji Abdullahi.  

  • Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
  • Atiku Ya Yi Murna, Ya Yi Marhaba Da Peter Obi A ADC

Haka kuma Abdullahi ya nuna damuwarsa game da zargin da ake yi wa ƴan majalisa na sauya dokar haraji wanda aka ƙaƙaba wa ƴan Nijeriya a wannan shekara, ya sava wa dimokuraɗyyar ƙasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

Ya zargi gwamnati da aiwatar da wasu ƙudirorin na ƙasashen ƙetare waɗanda ba su dace da tsarin mulkin ƙasar nan ba.

“Gwamnatin da za ta iya amicewa da dokar da aka yi wa cushe, me kake kiran irin wannan gwamnati?” ya tambaya.

Ya musanta cewa a cikin kasafin kuɗin 2026, yawan kuɗaɗen da za a kashe a wasu abubuwa marasa fifiko ya nuna cewa gwamnatin ta gaza. Ya ce saka irin wannan adadin a vangaren tsaro na cikin gida zai ba da sakamako mafi kyau fiye da ƙoƙarin tabbatar wa shugabannin ƙasashen waje cewa Nijeriya tana zaune lafiya.

“Ba su damu da yadda ‘yan Nijeriya ke ci gaba da mutuwa. Ba su damu cewa mutane na ci gaba da hallaka ba. Abin da suke so kawai shi ne, su sami fada a gaban Amurkawa,” in ji Abdullahi.

Mai magana da yawun ADC ya nuna damuwa kan yarjejeniyar fahimtar juna ta likitanci tsakanin Nijeriya da Amurka, wadda aka ruwaito an sanya hannu a kanta a ranar 19 ga Disamba, wanda ya yi iƙirarin cewa za ta bai wa Amurka ikon sarrafawa da rarraba kuɗaɗe sosai duk da cewa Nijeriya ce ke bayar da mafi girman gudummawar kuɗi.

“Babu ɗan Nijeriya da ya ga cikakkun bayanan wannan yarjejeiya” in ji shi, yana bayyana sharuɗɗan a matsayin abin mamaki yayin da ya yi tambayoyi game da ikon mallaka na ƙasa da ƙasa.

Tinubu
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Maniyyatan Nijeriya
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
'Yan Bindiga
Manyan Labarai

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

June 23, 2026
Next Post
Osimhen Ya Zura Ƙwallonsa Ta 50 A Galatasaray

Osimhen Ya Zura Ƙwallonsa Ta 50 A Galatasaray

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, Takwas Sun Jikkata Yayin Rikicin A Bauchi

An Kashe Mutum 2, Takwas Sun Jikkata Yayin Rikicin A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.