ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙwararru Sun Yi Watsi Da Shawarwarin Bankin Duniya Na Shigo Da Mai Fetur Zuwa Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
2 months ago

Dilalan man fetur da ƙwararru sun yi watsi da shawarwarin Bankin Duniya na shigo da mai zuwa Nijeriya don samun fa’ida ga masana’antar sarrafa man Dangote.

Idan za a iya tunawa dai, a ranar 7 ga Afrilu, Bankin Duniya ya ba da shawarar cewa Nijeriya ta fifita shigo da man fetur maimakon dogara da na ciki gida.

  • ’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa
  • Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
  • An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
  • Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
  • Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Bankin ya yi iƙirarin cewa man fetur da aka shigo da shi ya fi arha fiye da man fetur da ake samarwa a cikin gida Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Sai dai kuma shawarwarin Bankin Duniya sun haifar da cece-cuce.

Bayan kwanaki kaɗan, Bankin Duniya ya goge rahoton NDU daga rukunin yanar gizonsa kuma ya bayyana cewa ba shawararsu ba ce ta tabbatar da shigo da man fetur gaba ɗaya ba, amma wata babbar dabara ce da ta shafi gyare-gyare da kare haƙƙin masu amfani da man a Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

Bayan haka, bankin ya tasaya kan matsayinsa na baya kan sassaucin dokokin masana’antar mai ta ƙasa a Nijeriya.

“A game da Nijeriya, ya kamata a mayar da hankali wajen samar da tallafi ga mutane mafi rauni ta hanyar tsarin kariya na zamantakewa da ke aiki da kyau, kuma Bankin Duniya a shirye yake don ƙara tallafin da yake bayarwa a yanzu,” in ji Bankin Duniya a ranar Alhamis makon da ya wuce.

Masana makamashi sun soki matsayar Bankin Duniya, musamman ganin yadda man fetar ya tashi a kasuwan duniya sakamakon yaƙin Iran da Amurka da Izira’ila, wanda ya shiga mako na bakwai a ranar Talata.

An ruwaito cewa cibiyar inganta masana’antu masu zaman kansu, a cikin wata sanarwa da shugaban cibiyar, Dakta Muda Yusuf, ya fitar a ƙarshen mako, ya ce shawarwarin Bankin Duniya na shigo da fetur zuwa Nijeriya zai zama abin da ba zai haifar da ɗa mai ido ba.

Haka kuma, mai magana da yawun ƙungiyar masu mallakar tashoshin sarrafa mai a Nijeriya (CORAN), Eche Idoko, ya soki shawarwarin, yana mai cewa man fetur ƙasar yana da inganci fiye da wanda ake shigowa da shi.

Kazalika, ƙungiyar dillalan man fetur ta Nijeriya (PETROAN), a cikin wani bayani da shugabanta, Billy Gillis-Harry, ya fitar, ta goyi bayan Bankin Duniya kan dalilin gasa a sashen saukar da man fetur.

Sai dai kuma, ƙungiyar ta soki matakin manufar Nijeriya da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gabatar.

Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Taya Guelleh Murnar Sake Lashe Zaben Shugaban Djibouti

Xi Jinping Ya Taya Guelleh Murnar Sake Lashe Zaben Shugaban Djibouti

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.