ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙwararru Sun Yi Watsi Da Shawarwarin Bankin Duniya Na Shigo Da Mai Fetur Zuwa Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
3 months ago

Dilalan man fetur da ƙwararru sun yi watsi da shawarwarin Bankin Duniya na shigo da mai zuwa Nijeriya don samun fa’ida ga masana’antar sarrafa man Dangote.

Idan za a iya tunawa dai, a ranar 7 ga Afrilu, Bankin Duniya ya ba da shawarar cewa Nijeriya ta fifita shigo da man fetur maimakon dogara da na ciki gida.

  • CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai
  • Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
  • ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno
  • Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Bankin ya yi iƙirarin cewa man fetur da aka shigo da shi ya fi arha fiye da man fetur da ake samarwa a cikin gida Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Sai dai kuma shawarwarin Bankin Duniya sun haifar da cece-cuce.

Bayan kwanaki kaɗan, Bankin Duniya ya goge rahoton NDU daga rukunin yanar gizonsa kuma ya bayyana cewa ba shawararsu ba ce ta tabbatar da shigo da man fetur gaba ɗaya ba, amma wata babbar dabara ce da ta shafi gyare-gyare da kare haƙƙin masu amfani da man a Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

Bayan haka, bankin ya tasaya kan matsayinsa na baya kan sassaucin dokokin masana’antar mai ta ƙasa a Nijeriya.

“A game da Nijeriya, ya kamata a mayar da hankali wajen samar da tallafi ga mutane mafi rauni ta hanyar tsarin kariya na zamantakewa da ke aiki da kyau, kuma Bankin Duniya a shirye yake don ƙara tallafin da yake bayarwa a yanzu,” in ji Bankin Duniya a ranar Alhamis makon da ya wuce.

Masana makamashi sun soki matsayar Bankin Duniya, musamman ganin yadda man fetar ya tashi a kasuwan duniya sakamakon yaƙin Iran da Amurka da Izira’ila, wanda ya shiga mako na bakwai a ranar Talata.

An ruwaito cewa cibiyar inganta masana’antu masu zaman kansu, a cikin wata sanarwa da shugaban cibiyar, Dakta Muda Yusuf, ya fitar a ƙarshen mako, ya ce shawarwarin Bankin Duniya na shigo da fetur zuwa Nijeriya zai zama abin da ba zai haifar da ɗa mai ido ba.

Haka kuma, mai magana da yawun ƙungiyar masu mallakar tashoshin sarrafa mai a Nijeriya (CORAN), Eche Idoko, ya soki shawarwarin, yana mai cewa man fetur ƙasar yana da inganci fiye da wanda ake shigowa da shi.

Kazalika, ƙungiyar dillalan man fetur ta Nijeriya (PETROAN), a cikin wani bayani da shugabanta, Billy Gillis-Harry, ya fitar, ta goyi bayan Bankin Duniya kan dalilin gasa a sashen saukar da man fetur.

Sai dai kuma, ƙungiyar ta soki matakin manufar Nijeriya da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gabatar.

Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tattalin Arziki

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Taya Guelleh Murnar Sake Lashe Zaben Shugaban Djibouti

Xi Jinping Ya Taya Guelleh Murnar Sake Lashe Zaben Shugaban Djibouti

LABARAI MASU NASABA

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.