Dilalan man fetur da ƙwararru sun yi watsi da shawarwarin Bankin Duniya na shigo da mai zuwa Nijeriya don samun fa’ida ga masana’antar sarrafa man Dangote.
Idan za a iya tunawa dai, a ranar 7 ga Afrilu, Bankin Duniya ya ba da shawarar cewa Nijeriya ta fifita shigo da man fetur maimakon dogara da na ciki gida.
- Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
- Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
- Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
- ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP
- An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Bankin ya yi iƙirarin cewa man fetur da aka shigo da shi ya fi arha fiye da man fetur da ake samarwa a cikin gida Nijeriya.
Sai dai kuma shawarwarin Bankin Duniya sun haifar da cece-cuce.
Bayan kwanaki kaɗan, Bankin Duniya ya goge rahoton NDU daga rukunin yanar gizonsa kuma ya bayyana cewa ba shawararsu ba ce ta tabbatar da shigo da man fetur gaba ɗaya ba, amma wata babbar dabara ce da ta shafi gyare-gyare da kare haƙƙin masu amfani da man a Nijeriya.
Bayan haka, bankin ya tasaya kan matsayinsa na baya kan sassaucin dokokin masana’antar mai ta ƙasa a Nijeriya.
“A game da Nijeriya, ya kamata a mayar da hankali wajen samar da tallafi ga mutane mafi rauni ta hanyar tsarin kariya na zamantakewa da ke aiki da kyau, kuma Bankin Duniya a shirye yake don ƙara tallafin da yake bayarwa a yanzu,” in ji Bankin Duniya a ranar Alhamis makon da ya wuce.
Masana makamashi sun soki matsayar Bankin Duniya, musamman ganin yadda man fetar ya tashi a kasuwan duniya sakamakon yaƙin Iran da Amurka da Izira’ila, wanda ya shiga mako na bakwai a ranar Talata.
An ruwaito cewa cibiyar inganta masana’antu masu zaman kansu, a cikin wata sanarwa da shugaban cibiyar, Dakta Muda Yusuf, ya fitar a ƙarshen mako, ya ce shawarwarin Bankin Duniya na shigo da fetur zuwa Nijeriya zai zama abin da ba zai haifar da ɗa mai ido ba.
Haka kuma, mai magana da yawun ƙungiyar masu mallakar tashoshin sarrafa mai a Nijeriya (CORAN), Eche Idoko, ya soki shawarwarin, yana mai cewa man fetur ƙasar yana da inganci fiye da wanda ake shigowa da shi.
Kazalika, ƙungiyar dillalan man fetur ta Nijeriya (PETROAN), a cikin wani bayani da shugabanta, Billy Gillis-Harry, ya fitar, ta goyi bayan Bankin Duniya kan dalilin gasa a sashen saukar da man fetur.
Sai dai kuma, ƙungiyar ta soki matakin manufar Nijeriya da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gabatar.















Discussion about this post