ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Ƴan Bindiga Sun Hana Manoman Sakkwato Zuwa Gonakinsu, Sun Ƙaƙaba Sabbin Haraji

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
3 weeks ago
Manoma

Aƙalla mazauna ƙauyuka 26 da ke Ƙaramar Hukumar Sabon Birni ta Jihar Sakkwato sun fara tara kuɗaɗe domin biyan sabbin harajin da ƴan bindiga suka ƙaƙaba musu, bayan da suka hana su zuwa gonakinsu gabanin fara noman damina.

Mazauna yankin sun shaida cewa ƙungiyoyin ƴan bindigar sun ba su wa’adin kwanaki uku, tare da gargaɗin cewa babu wanda zai je gona har sai an biya kuɗin harajin da suka buƙata.

Daga cikin ƙauyukan da abin ya shafa akwai Garin Faji, Cina Barka, Zululu, Dan Gari, Garin Maigayya, Gardi, Katsira, Garin Baushe, Sulmawa, Zakin Ganga, Dan Kware, Garje, Dogon Faru, Son Allah, Garin Galadima, Kafchi, Matabaya, Garin Labo, Zango, Kaifin Aska, Tsauna Dogo, Tudun Wada, Rambadawa, Ga Itace, Nasarawa da Garin Idi.

ADVERTISEMENT

Wani mazaunin yankin ya ce ƴan bindigar sun yi barazanar kashewa ko sace duk wanda suka kama yana noma a wannan lokacin.

“Sun ba ƙauyukan kwanaki uku. Sun ce babu wanda zai je gona har sai an biya kuɗin. Duk wanda aka kama yana noma za a kashe shi ko kuma a sace shi, kuma ba zai samu ƴanci ba sai ya biya kuɗin fansa na Naira 500,000,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Takwas A Katsina

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

Ya ƙara da cewa mazauna yankunan sun riga sun fara tara kuɗi domin biyan abin da aka nema.

Wani mazaunin ƙauyen Zululu, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce yana shirin zuwa gonarsa ranar Juma’a ne lokacin da ya samu labarin wannan umarni.

“Yawanci suna neman tsakanin Naira miliyan 4 zuwa Naira miliyan 6 daga kowace al’umma. Mazauna ƙauyuka suna bayar da gudummawa gwargwadon ƙarfinsu. Wasu gidaje suna biyan Naira 1,500 ko Naira 2,000, yayin da a wasu ƙauyuka manoma ke biyan har Naira 5,000 kowannensu,” ya bayyana.

Wata majiya daga Garin Idi ta ce lokacin da ƴan bindigar suka ga ana jinkirin tara kuɗin, sai suka kai hari ƙauyen inda suka yi garkuwa da kusan mutum 20 a safiyar ranar Juma’a.

“Daga baya sun sanar da shugabannin al’umma cewa dole ne a biya Naira 600,000 kafin a saki waɗanda aka sace. An tara kuɗin kuma aka biya, wanda ya sa aka saki mutanen a ranar Juma’a,” in ji shi.

Sai dai ya ce har yanzu akwai mutum biyar da ke hannun ƴan bindigar.

“Har yanzu suna riƙe da mutum biyar. Sun ce ba za su sake su ba har sai an biya harajin. Ko bayan an yi noma ma, suna iya hana mutane girbi har sai an sake biyan wani kuɗi,” a cewarsa.

Ya kuma yi zargin cewa bayan girbi, manoma kan kasance tilas su ba ƴan bindigar wani kaso na amfanin gonarsu kafin a ba su damar ajiye amfanin a rumbunansu.

“Duk shekara bayan girbi, suna karbar wani bangare na amfanin gona daga manoma kafin su ba su damar adanawa. Wannan ya zama wata babbar matsala ga al’ummominmu,” in ji shi.

Da aka tuntubi jami’in hulɗa da jama’a na Rundunar Ƴansandan Jihar Sakkwato, DSP Ahmad Rufai, ya ce rundunar ba ta da masaniya kan lamarin.

“Ba mu da labarin irin wannan abu. Yawanci al’ummomi ba sa kai irin waɗannan rahotanni ga hukumomin tsaro,” in ji shi.

Ƙoƙarin jin ta bakin gwamnatin Jihar Sakkwato bai yi nasara ba, domin saƙonnin da aka aika wa kakakin gwamnan da mai ba gwamna shawara kan harkokin tsaro ba su samu amsa ba har zuwa lokacin kammala wannan rahoto.

Manoma
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas
Manoma
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Takwas A Katsina
  • Sulaiman
    Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

MASU ALAKA

Ta’addanci
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Takwas A Katsina

July 9, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’
Tsaro

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Next Post
Hukumar NEPZA Ta Tabbatar Wa Da Masu Zuba Jari Goyon Bayanta

Hukumar NEPZA Ta Tabbatar Wa Da Masu Zuba Jari Goyon Bayanta

LABARAI MASU NASABA

Ta’addanci

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Takwas A Katsina

July 9, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Auto Draft

TCN Ta Kammala Gyaran Layin Wutar Lantarkin Zaria–Funtua 132kV

July 9, 2026
Auto Draft

DSS Ta Kama ‘Yar Jarida Zainab Sodiq Kan Zargin Mallakar Drone Ba Tare da Cikakkun Takardu ba

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

July 9, 2026
Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

July 9, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A  Jihar Benuwai

’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A Jihar Benuwai

July 9, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.