ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Ƴan Bindiga Sun Hana Manoman Sakkwato Zuwa Gonakinsu, Sun Ƙaƙaba Sabbin Haraji

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
1 hour ago
Manoma

Aƙalla mazauna ƙauyuka 26 da ke Ƙaramar Hukumar Sabon Birni ta Jihar Sakkwato sun fara tara kuɗaɗe domin biyan sabbin harajin da ƴan bindiga suka ƙaƙaba musu, bayan da suka hana su zuwa gonakinsu gabanin fara noman damina.

Mazauna yankin sun shaida cewa ƙungiyoyin ƴan bindigar sun ba su wa’adin kwanaki uku, tare da gargaɗin cewa babu wanda zai je gona har sai an biya kuɗin harajin da suka buƙata.

Daga cikin ƙauyukan da abin ya shafa akwai Garin Faji, Cina Barka, Zululu, Dan Gari, Garin Maigayya, Gardi, Katsira, Garin Baushe, Sulmawa, Zakin Ganga, Dan Kware, Garje, Dogon Faru, Son Allah, Garin Galadima, Kafchi, Matabaya, Garin Labo, Zango, Kaifin Aska, Tsauna Dogo, Tudun Wada, Rambadawa, Ga Itace, Nasarawa da Garin Idi.

ADVERTISEMENT

Wani mazaunin yankin ya ce ƴan bindigar sun yi barazanar kashewa ko sace duk wanda suka kama yana noma a wannan lokacin.

“Sun ba ƙauyukan kwanaki uku. Sun ce babu wanda zai je gona har sai an biya kuɗin. Duk wanda aka kama yana noma za a kashe shi ko kuma a sace shi, kuma ba zai samu ƴanci ba sai ya biya kuɗin fansa na Naira 500,000,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NEPZA Ta Tabbatar Wa Da Masu Zuba Jari Goyon Bayanta

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

Ya ƙara da cewa mazauna yankunan sun riga sun fara tara kuɗi domin biyan abin da aka nema.

Wani mazaunin ƙauyen Zululu, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce yana shirin zuwa gonarsa ranar Juma’a ne lokacin da ya samu labarin wannan umarni.

“Yawanci suna neman tsakanin Naira miliyan 4 zuwa Naira miliyan 6 daga kowace al’umma. Mazauna ƙauyuka suna bayar da gudummawa gwargwadon ƙarfinsu. Wasu gidaje suna biyan Naira 1,500 ko Naira 2,000, yayin da a wasu ƙauyuka manoma ke biyan har Naira 5,000 kowannensu,” ya bayyana.

Wata majiya daga Garin Idi ta ce lokacin da ƴan bindigar suka ga ana jinkirin tara kuɗin, sai suka kai hari ƙauyen inda suka yi garkuwa da kusan mutum 20 a safiyar ranar Juma’a.

“Daga baya sun sanar da shugabannin al’umma cewa dole ne a biya Naira 600,000 kafin a saki waɗanda aka sace. An tara kuɗin kuma aka biya, wanda ya sa aka saki mutanen a ranar Juma’a,” in ji shi.

Sai dai ya ce har yanzu akwai mutum biyar da ke hannun ƴan bindigar.

“Har yanzu suna riƙe da mutum biyar. Sun ce ba za su sake su ba har sai an biya harajin. Ko bayan an yi noma ma, suna iya hana mutane girbi har sai an sake biyan wani kuɗi,” a cewarsa.

Ya kuma yi zargin cewa bayan girbi, manoma kan kasance tilas su ba ƴan bindigar wani kaso na amfanin gonarsu kafin a ba su damar ajiye amfanin a rumbunansu.

“Duk shekara bayan girbi, suna karbar wani bangare na amfanin gona daga manoma kafin su ba su damar adanawa. Wannan ya zama wata babbar matsala ga al’ummominmu,” in ji shi.

Da aka tuntubi jami’in hulɗa da jama’a na Rundunar Ƴansandan Jihar Sakkwato, DSP Ahmad Rufai, ya ce rundunar ba ta da masaniya kan lamarin.

“Ba mu da labarin irin wannan abu. Yawanci al’ummomi ba sa kai irin waɗannan rahotanni ga hukumomin tsaro,” in ji shi.

Ƙoƙarin jin ta bakin gwamnatin Jihar Sakkwato bai yi nasara ba, domin saƙonnin da aka aika wa kakakin gwamnan da mai ba gwamna shawara kan harkokin tsaro ba su samu amsa ba har zuwa lokacin kammala wannan rahoto.

Manoma
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Matsalar Tsaro:Kashi 60 Na Masana’antu A Arewa Maso Gabas Sun Durƙushe
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Shekarar Musulunci: Tinubu Ya Yi Kira Da A Nuna Kyakkyawan Kishin Ƙasa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Iran Ta Yi Wa Sansanonin Sojin Amurka 20 Mummunar Barna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno
Manoma
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Hukumar NEPZA Ta Tabbatar Wa Da Masu Zuba Jari Goyon Bayanta
  • Sulaiman
    Matsalar Tsaro:Kashi 60 Na Masana’antu A Arewa Maso Gabas Sun Durƙushe
  • Sulaiman
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • Sulaiman
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina

MASU ALAKA

Hukumar NEPZA Ta Tabbatar Wa Da Masu Zuba Jari Goyon Bayanta
Labarai

Hukumar NEPZA Ta Tabbatar Wa Da Masu Zuba Jari Goyon Bayanta

June 19, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

June 19, 2026
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su
Rahotonni

Matsalar Tsaro:Kashi 60 Na Masana’antu A Arewa Maso Gabas Sun Durƙushe

June 19, 2026
Next Post
Hukumar NEPZA Ta Tabbatar Wa Da Masu Zuba Jari Goyon Bayanta

Hukumar NEPZA Ta Tabbatar Wa Da Masu Zuba Jari Goyon Bayanta

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NEPZA Ta Tabbatar Wa Da Masu Zuba Jari Goyon Bayanta

Hukumar NEPZA Ta Tabbatar Wa Da Masu Zuba Jari Goyon Bayanta

June 19, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Ƴan Bindiga Sun Hana Manoman Sakkwato Zuwa Gonakinsu, Sun Ƙaƙaba Sabbin Haraji

June 19, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

June 19, 2026
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

Matsalar Tsaro:Kashi 60 Na Masana’antu A Arewa Maso Gabas Sun Durƙushe

June 19, 2026
Kotun Ƙoli Za Ta Yanke Hukunci Kan Rikicin PDP Da ADC Yau

Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina

June 19, 2026
Tinubu

Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina

June 19, 2026
Kawayen amarya

Matsalar Tsaro:Yadda Sabbin Matakan Gwamnati Ke Shafar Walwalar Al’ummar Jihar Katsina

June 19, 2026
Manzon Allah

Falalar Haɗa Basmala da Suratul Fatiha

June 19, 2026
Yadda Ɗiyata Tilo Ta Mutu A Wata Makarantar Sakandire A Kano – Mahaifiya

Yadda Ɗiyata Tilo Ta Mutu A Wata Makarantar Sakandire A Kano – Mahaifiya

June 19, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Majalisar Wakilai Ta Fara Yunƙurin Gyaran Dokokin Soja

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.