Aƙalla mazauna ƙauyuka 26 da ke Ƙaramar Hukumar Sabon Birni ta Jihar Sakkwato sun fara tara kuɗaɗe domin biyan sabbin harajin da ƴan bindiga suka ƙaƙaba musu, bayan da suka hana su zuwa gonakinsu gabanin fara noman damina.
Mazauna yankin sun shaida cewa ƙungiyoyin ƴan bindigar sun ba su wa’adin kwanaki uku, tare da gargaɗin cewa babu wanda zai je gona har sai an biya kuɗin harajin da suka buƙata.
Daga cikin ƙauyukan da abin ya shafa akwai Garin Faji, Cina Barka, Zululu, Dan Gari, Garin Maigayya, Gardi, Katsira, Garin Baushe, Sulmawa, Zakin Ganga, Dan Kware, Garje, Dogon Faru, Son Allah, Garin Galadima, Kafchi, Matabaya, Garin Labo, Zango, Kaifin Aska, Tsauna Dogo, Tudun Wada, Rambadawa, Ga Itace, Nasarawa da Garin Idi.
Wani mazaunin yankin ya ce ƴan bindigar sun yi barazanar kashewa ko sace duk wanda suka kama yana noma a wannan lokacin.
“Sun ba ƙauyukan kwanaki uku. Sun ce babu wanda zai je gona har sai an biya kuɗin. Duk wanda aka kama yana noma za a kashe shi ko kuma a sace shi, kuma ba zai samu ƴanci ba sai ya biya kuɗin fansa na Naira 500,000,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa mazauna yankunan sun riga sun fara tara kuɗi domin biyan abin da aka nema.
Wani mazaunin ƙauyen Zululu, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce yana shirin zuwa gonarsa ranar Juma’a ne lokacin da ya samu labarin wannan umarni.
“Yawanci suna neman tsakanin Naira miliyan 4 zuwa Naira miliyan 6 daga kowace al’umma. Mazauna ƙauyuka suna bayar da gudummawa gwargwadon ƙarfinsu. Wasu gidaje suna biyan Naira 1,500 ko Naira 2,000, yayin da a wasu ƙauyuka manoma ke biyan har Naira 5,000 kowannensu,” ya bayyana.
Wata majiya daga Garin Idi ta ce lokacin da ƴan bindigar suka ga ana jinkirin tara kuɗin, sai suka kai hari ƙauyen inda suka yi garkuwa da kusan mutum 20 a safiyar ranar Juma’a.
“Daga baya sun sanar da shugabannin al’umma cewa dole ne a biya Naira 600,000 kafin a saki waɗanda aka sace. An tara kuɗin kuma aka biya, wanda ya sa aka saki mutanen a ranar Juma’a,” in ji shi.
Sai dai ya ce har yanzu akwai mutum biyar da ke hannun ƴan bindigar.
“Har yanzu suna riƙe da mutum biyar. Sun ce ba za su sake su ba har sai an biya harajin. Ko bayan an yi noma ma, suna iya hana mutane girbi har sai an sake biyan wani kuɗi,” a cewarsa.
Ya kuma yi zargin cewa bayan girbi, manoma kan kasance tilas su ba ƴan bindigar wani kaso na amfanin gonarsu kafin a ba su damar ajiye amfanin a rumbunansu.
“Duk shekara bayan girbi, suna karbar wani bangare na amfanin gona daga manoma kafin su ba su damar adanawa. Wannan ya zama wata babbar matsala ga al’ummominmu,” in ji shi.
Da aka tuntubi jami’in hulɗa da jama’a na Rundunar Ƴansandan Jihar Sakkwato, DSP Ahmad Rufai, ya ce rundunar ba ta da masaniya kan lamarin.
“Ba mu da labarin irin wannan abu. Yawanci al’ummomi ba sa kai irin waɗannan rahotanni ga hukumomin tsaro,” in ji shi.
Ƙoƙarin jin ta bakin gwamnatin Jihar Sakkwato bai yi nasara ba, domin saƙonnin da aka aika wa kakakin gwamnan da mai ba gwamna shawara kan harkokin tsaro ba su samu amsa ba har zuwa lokacin kammala wannan rahoto.















Discussion about this post