ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Kan Tawagar Biki, Sun Kashe Mutane 2, Sun Sace Wasu

by Abubakar Sulaiman
5 months ago
Bindiga

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Wasu da ake zargin ƴan bindiga ne sun kai hari kan tawagar masu halartar bikin aure a unguwar Nagunda da ke ƙaramar hukumar Kankara a Jihar Katsina, inda suka kashe aƙalla mutum biyu tare da jikkata wasu da dama, ciki har da amaryar. Harin, wanda ya faru a daren Lahadi, ya kuma kai ga sace wasu baƙin bikin da har yanzu ba a tantance adadinsu ba, kamar yadda majiyoyi a yankin suka tabbatar.

Wata majiyar tsaro ta bayyana cewa an shiga firgici a yankin bayan da aka ji ƙarar harbe-harbe mai yawa lokacin da maharan suka mamaye unguwar. “Har zuwa safiyar Litinin, iyalai na ci gaba da ƙoƙarin tantance adadin mutanen da aka sace,” in ji majiyar. Lamarin ya jefa al’umma cikin fargaba, yayin da ake ci gaba da neman bayanai kan halin da waɗanda aka sace suke ciki.

  • Gwamnatin Katsina Ta Bayyana Dalilin Sakin Mutane 70 Da Ake Zargi Da Ta’addanci
  • Hare-haren ‘Yan Bindiga: An Sake Buɗe Makarantu A Kebbi Da Kwara

Harin ya zo ne a daidai lokacin da gwamnatin Jihar Katsina ke ƙoƙarin ƙarfafa yarjejeniyar zaman lafiya da ta ce tayi da ita da ’yan bindigar da suka tuba. Kwamishinan Tsaron Ciki da Harkokin Gida na jihar, Dokta Nasir Mu’azu, ya sha kare matakin sakin wasu mutane 70 da ake zargi da laifukan ’yan bindiga, yana mai cewa matakin na daga cikin dabarun gina amincewa domin dorewar zaman lafiya a yankunan da ke fama da rashin tsaro.

ADVERTISEMENT

Mu’azu ya ce yarjejeniyar zaman lafiyar ta shafi ƙananan hukumomi sama da 15, kuma har ta haifar da sakamako, ciki har da sakin kusan mutum 1,000 da aka sace a hare-haren baya. Sai dai duk da bayanan gwamnati, harin na Kankara ya sake tayar da muhawara a tsakanin jama’a, inda wasu ke nuna damuwa cewa irin waɗannan hare-hare na iya tauye adalci ga wadanda aka zalunta da ƙarfafar aikata laifi, yayin da wasu ke jaddada cewa tattaunawa da sassauci ne kaɗai hanyar samun zaman lafiya mai ɗorewa.

Bindiga
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje
  • Abubakar Sulaiman
    Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Next Post
Hadin Gwiwa Tsakanin Canada Da Sin Zai Iya Kai Su Ga Samun Ci Gaba Cikin Zaman Lafiya Da Wadata

Hadin Gwiwa Tsakanin Canada Da Sin Zai Iya Kai Su Ga Samun Ci Gaba Cikin Zaman Lafiya Da Wadata

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.