Wasu da ake zargin ƴan bindiga ne sun kai hari kan tawagar masu halartar bikin aure a unguwar Nagunda da ke ƙaramar hukumar Kankara a Jihar Katsina, inda suka kashe aƙalla mutum biyu tare da jikkata wasu da dama, ciki har da amaryar. Harin, wanda ya faru a daren Lahadi, ya kuma kai ga sace wasu baƙin bikin da har yanzu ba a tantance adadinsu ba, kamar yadda majiyoyi a yankin suka tabbatar.
Wata majiyar tsaro ta bayyana cewa an shiga firgici a yankin bayan da aka ji ƙarar harbe-harbe mai yawa lokacin da maharan suka mamaye unguwar. “Har zuwa safiyar Litinin, iyalai na ci gaba da ƙoƙarin tantance adadin mutanen da aka sace,” in ji majiyar. Lamarin ya jefa al’umma cikin fargaba, yayin da ake ci gaba da neman bayanai kan halin da waɗanda aka sace suke ciki.
- Gwamnatin Katsina Ta Bayyana Dalilin Sakin Mutane 70 Da Ake Zargi Da Ta’addanci
- Hare-haren ‘Yan Bindiga: An Sake Buɗe Makarantu A Kebbi Da Kwara
Harin ya zo ne a daidai lokacin da gwamnatin Jihar Katsina ke ƙoƙarin ƙarfafa yarjejeniyar zaman lafiya da ta ce tayi da ita da ’yan bindigar da suka tuba. Kwamishinan Tsaron Ciki da Harkokin Gida na jihar, Dokta Nasir Mu’azu, ya sha kare matakin sakin wasu mutane 70 da ake zargi da laifukan ’yan bindiga, yana mai cewa matakin na daga cikin dabarun gina amincewa domin dorewar zaman lafiya a yankunan da ke fama da rashin tsaro.
Mu’azu ya ce yarjejeniyar zaman lafiyar ta shafi ƙananan hukumomi sama da 15, kuma har ta haifar da sakamako, ciki har da sakin kusan mutum 1,000 da aka sace a hare-haren baya. Sai dai duk da bayanan gwamnati, harin na Kankara ya sake tayar da muhawara a tsakanin jama’a, inda wasu ke nuna damuwa cewa irin waɗannan hare-hare na iya tauye adalci ga wadanda aka zalunta da ƙarfafar aikata laifi, yayin da wasu ke jaddada cewa tattaunawa da sassauci ne kaɗai hanyar samun zaman lafiya mai ɗorewa.















Discussion about this post