Kwamishinan ƴansandan da ke kula da zaɓen gwamnan jihar Osun, Erale Samuel Etaifo, ya bayyana cewa an tsare kusan mutane 100 a tsawon wata guda da ya gabata, bisa zargin yunkurin kawo cikas ga gudanar da zaɓen gwamnan jihar. Etaifo ya bayyana hakan ne a ranar Asabar, yayin da yake zantawa da gidan talabijin na Channels.
Kwamishinan ya ce an kamo waɗanda ake zargin ne a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin daƙile rikici da sauran matsaloli a lokacin zaɓen. Ya kara da cewa, wasu daga cikin waɗanda aka kama ɗin sun shigo jihar Osun ne daga jihohi makwabta da suka haɗa da Ondo da Ekiti, da nufin haddasa rikici. Sai dai kuma, kwamishinan ya tabbatar da cewa ba a kama kowa ba a ranar zaɓen saboda tashin hankali, inda ya bayyana cewa babu dalilin yin hakan ya zuwa lokacin tattaunawar.
Da yake mayar da martani kan zargin da Gwamna Ademola Adeleke ya yi game da wani ɗan sanda da ake kira “London” da aka turo daga Fatakwal, Etaifo ya fayyace cewa Sufeto-Janar na Ƴansanda yana da hurumin tura jami’ai masu aiki zuwa kowane lungu na ƙasar nan. Ya ce an tura manyan jami’an ‘yansanda biyu zuwa yankin Ede don ƙarfafa tsaro, domin an gano cewa yankin na ɗaya daga cikin wuraren da ake tunanin samun tashin hankali a jihar.
A wani labarin kuma, Gwamna Adeleke, jim kaɗan bayan ya kaɗa ƙuri’arsa, ya nuna ƙwarin gwiwar samun nasara a zaɓen tare da yin kira ga masu zaɓe da su fito kwansu da kwarkwatarsu don kaɗa ƙuri’a tare da kare ta.
Haka kuma ya zargi wasu jami’an ‘yansanda da tsoratar da magoya bayansa a Modakeke da wasu yankunan jihar, tare da gargaɗin cewa ana ci gaba da rarraba takardun zaɓe na bogi da nufin yaudarar masu zaɓe a wasu mazaɓun.














