ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Mahangar ECOWAS Kan Zaben Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
ECOWAS

Kungiyar Bunkasa da Tallalin Arzikin Kasahen Yammacin Afirka (ECOWAS), karkashin tawagar kula da shirye-shiryen zabe a Nijeriya ta bayyana mahangarta game da zaben 2023 da za a yi a Nijeriya.

Kamar yadda tawagar kungiyar dai ta bayyana, zaben na 2023 na iya shafar daukacin yankin Yammacin Afirka.Tawagar ta bayyana hakan ne lokacin da ta ziyarci shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu a Abuja a farkon makon nan.

  • Ya Kamata Amurka Ta Soke Takunkumi Idan Tana Son Taimakawa Afirka
  • Ta’addanci Ya Zama Tarihi, Nijeriya Na Cikin Aminci – Lai Muhammad

Tawagardai ta ziyarci shugaban ne a karkashin jagorancin Tsohon Shugaban Hukumar zaben kasar Ghana, Kwadwo Afari-Gyan.

ADVERTISEMENT

Da yake jawabi a madadin wakilan ,Daraktan Harkokin Siyasa na ECOWAS, Remi Ajiewa ya bayyana cewa yankin yammacin Afirka na neman ganin an samu sahihin zabe a Nijeriya a 2023, domin shugaban Nijeriya yana matukar taka muhimmiyar rawa a yankin.

“Mun san irin muhimmancin Nijeriya a yankin Yammacin Afirka, domin idan Nijeriya ta yi atishawa sai ya shafi daukacin Yammacin Afirka, saboda haka ba ma fatan hakan ya faru.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

“Mun zo ne domin mu saurari bayaninka da kuma ganin wuraren da ake samun kalubale domin mu hada rahoto a kai.”

Mista Ajibewa ya kara da cewa sun zo Nijeriya domin hada bincike gabanin zaben 2023 kamar yadda suka saka ido a karkashin ECOWAS a zaben Nijeriyana shekarar 2021.

Ya ce sashe na 11 da 12 da kuma13 na dokokin kungiyar ECOWAS ya tanadi cewa idan za a yi zabe za a hada rahoto ga dukkan mambobin kungiyar, musamman ma zaben shugaban kasa.

“Wannan ne ya sa muka zo Nijeriya wanda muka fara ziyartar shalkwatar ECOWAS tare da tattaunawa da shagabannin kungiyar.

“Bayan nan mun ziyarci ma’aikatan harkokin waje a wannan safiya da sufetan ‘yansanda na kasa da wasu daga cikin kungiyoyin fararen hula da kuma INEC.

“Ko shakka babau, dalilin da ya sa muke gudanar da irin wannan lamarishi ne, INEC kawarmu ce kuma wasu abubuwa da muke ji mukan tattauna domin a samun masalaha.

“Bayan mun tashi daga nan, za mu ziyarci dukkan sassan Nijeriya domin tattaunawa da kwamishinonin zabe. Sannan za mu ziyarci hukumomin tsaro da shugabannin gargajiya da kuma shugabannin addinai.

“Ba za mu manta da jam’iyyun siyasa ba wajen ganin sun gudanar da ayyukansu kamar yadda tsarin Mulki ya shardanta musu. Haka kuma za mu

gana da kafafen yada labarai kan rawarda suke takawa,” in ji shi.

Mista Ajibewa ya kara da cewa ba wannan ne karon farko da tawagar ta ziyarci Nijeriya ba, domin kuwa sun saba zuwa a duk lokacin da za a gudanar da zabe a kasar ciki har da na 2019.

Da yake jawabi, Shugaban INEC, Farfesa Yakubu ya bayyana cewa hukumarsa ta gayyaci kungiyoyin kasashen duniya domin sa ido a wannan zabe.

Ya kara da cewa wannan ziyarar ta masu sa ido na kasa da kasa tana kara wa hukumar kwarin gwiwa.

“Masu sa ido kan zabe suna da matukar muhimmanci wajen tabbatar da gabin an gudanar da sahihin zabe. A ko da yaushe muna amfanuwa da masu saka ido na kungiyar ECOWAS.

“Alal misali, mun zo ne domin gudanar da bincike, za mu ji daga wurinku irin abubuwan da kuka gano da za su taimaka mana wajen shirye-shiryenzabe.

“Ina bukatar amsar rahotonku wanda za ku kammala a tsakanin watan Fabrairun zuwa Maris, domin mu kara samun ilimi daga ciki,” in ji shi.

Shugaban hukumar INEC ya tabbatar wa tawagar ECOWAS cewaza a yi amfani da na’urorin zamani a zaben Nijeriya na 2023.

Mista Yakubu ya yaba wa tawagar ECOWAS wajen kokarin ganin an gudanar da sahihin zabe a Nijeriya.

Ya ce akwai bukatar ceto dimokuradiyya a dukkan yankunan yammacin Afirka ciki har da kasashen Mali da Burkina da kuma Guinea.

ECOWAS
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

MASU ALAKA

Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Manyan Labarai

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo
Manyan Labarai

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Yi Ta’aziyyar ’Ya’yan Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi da Suka Rasu a Hatsarin Mota

July 6, 2026
Next Post
PDP Ta Yi Satar Amsa Daga Manufofin Buhari – Tinubu

PDP Ta Yi Satar Amsa Daga Manufofin Buhari – Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.