ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Mahangar ECOWAS Kan Zaben Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
ECOWAS

Kungiyar Bunkasa da Tallalin Arzikin Kasahen Yammacin Afirka (ECOWAS), karkashin tawagar kula da shirye-shiryen zabe a Nijeriya ta bayyana mahangarta game da zaben 2023 da za a yi a Nijeriya.

Kamar yadda tawagar kungiyar dai ta bayyana, zaben na 2023 na iya shafar daukacin yankin Yammacin Afirka.Tawagar ta bayyana hakan ne lokacin da ta ziyarci shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu a Abuja a farkon makon nan.

  • Ya Kamata Amurka Ta Soke Takunkumi Idan Tana Son Taimakawa Afirka
  • Ta’addanci Ya Zama Tarihi, Nijeriya Na Cikin Aminci – Lai Muhammad

Tawagardai ta ziyarci shugaban ne a karkashin jagorancin Tsohon Shugaban Hukumar zaben kasar Ghana, Kwadwo Afari-Gyan.

ADVERTISEMENT

Da yake jawabi a madadin wakilan ,Daraktan Harkokin Siyasa na ECOWAS, Remi Ajiewa ya bayyana cewa yankin yammacin Afirka na neman ganin an samu sahihin zabe a Nijeriya a 2023, domin shugaban Nijeriya yana matukar taka muhimmiyar rawa a yankin.

“Mun san irin muhimmancin Nijeriya a yankin Yammacin Afirka, domin idan Nijeriya ta yi atishawa sai ya shafi daukacin Yammacin Afirka, saboda haka ba ma fatan hakan ya faru.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

“Mun zo ne domin mu saurari bayaninka da kuma ganin wuraren da ake samun kalubale domin mu hada rahoto a kai.”

Mista Ajibewa ya kara da cewa sun zo Nijeriya domin hada bincike gabanin zaben 2023 kamar yadda suka saka ido a karkashin ECOWAS a zaben Nijeriyana shekarar 2021.

Ya ce sashe na 11 da 12 da kuma13 na dokokin kungiyar ECOWAS ya tanadi cewa idan za a yi zabe za a hada rahoto ga dukkan mambobin kungiyar, musamman ma zaben shugaban kasa.

“Wannan ne ya sa muka zo Nijeriya wanda muka fara ziyartar shalkwatar ECOWAS tare da tattaunawa da shagabannin kungiyar.

“Bayan nan mun ziyarci ma’aikatan harkokin waje a wannan safiya da sufetan ‘yansanda na kasa da wasu daga cikin kungiyoyin fararen hula da kuma INEC.

“Ko shakka babau, dalilin da ya sa muke gudanar da irin wannan lamarishi ne, INEC kawarmu ce kuma wasu abubuwa da muke ji mukan tattauna domin a samun masalaha.

“Bayan mun tashi daga nan, za mu ziyarci dukkan sassan Nijeriya domin tattaunawa da kwamishinonin zabe. Sannan za mu ziyarci hukumomin tsaro da shugabannin gargajiya da kuma shugabannin addinai.

“Ba za mu manta da jam’iyyun siyasa ba wajen ganin sun gudanar da ayyukansu kamar yadda tsarin Mulki ya shardanta musu. Haka kuma za mu

gana da kafafen yada labarai kan rawarda suke takawa,” in ji shi.

Mista Ajibewa ya kara da cewa ba wannan ne karon farko da tawagar ta ziyarci Nijeriya ba, domin kuwa sun saba zuwa a duk lokacin da za a gudanar da zabe a kasar ciki har da na 2019.

Da yake jawabi, Shugaban INEC, Farfesa Yakubu ya bayyana cewa hukumarsa ta gayyaci kungiyoyin kasashen duniya domin sa ido a wannan zabe.

Ya kara da cewa wannan ziyarar ta masu sa ido na kasa da kasa tana kara wa hukumar kwarin gwiwa.

“Masu sa ido kan zabe suna da matukar muhimmanci wajen tabbatar da gabin an gudanar da sahihin zabe. A ko da yaushe muna amfanuwa da masu saka ido na kungiyar ECOWAS.

“Alal misali, mun zo ne domin gudanar da bincike, za mu ji daga wurinku irin abubuwan da kuka gano da za su taimaka mana wajen shirye-shiryenzabe.

“Ina bukatar amsar rahotonku wanda za ku kammala a tsakanin watan Fabrairun zuwa Maris, domin mu kara samun ilimi daga ciki,” in ji shi.

Shugaban hukumar INEC ya tabbatar wa tawagar ECOWAS cewaza a yi amfani da na’urorin zamani a zaben Nijeriya na 2023.

Mista Yakubu ya yaba wa tawagar ECOWAS wajen kokarin ganin an gudanar da sahihin zabe a Nijeriya.

Ya ce akwai bukatar ceto dimokuradiyya a dukkan yankunan yammacin Afirka ciki har da kasashen Mali da Burkina da kuma Guinea.

ECOWAS
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
PDP Ta Yi Satar Amsa Daga Manufofin Buhari – Tinubu

PDP Ta Yi Satar Amsa Daga Manufofin Buhari – Tinubu

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.