ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Ana Zazzafar Muhawara Kan Muslim-muslim Tiket A Takarar Tinubu

by Leadership Hausa
6 months ago
2027

Masu tsara dabarun siyasa na arewa da ra’ayoyin shugabannin sun cire yiwuwar ɗaukar Bishop Mathew Hassan Kukah, a matsayin mai yiwuwa ya maye gurbin mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima a zaven 2027.

Wani yunƙuri na baya-bayan nan, wanda ake cewa Amurka ta tayar, ya tayar da zazzafar da muhawara game da tikitin Musulmi-Musulmi da Shugaba ƙasa, Bola Tinubu ya yi amfani da shi a zaven 2023.

Shugaba Tinubu ya yi takara da Sanata Shettima a cikin tsarin Musulmi-Musulmi tiket, wanda wasu shugabannin Kiristoci a ƙasar suka yi adawa da shi.

ADVERTISEMENT

Amma adawar ta ɗan ragu bayan manyan kamfen-kamfen da suka jaddada halayen Tinubu na juriya ga addini da kuma zaman lafiya na addinai da ke akwai a yamma maso kudu, inda ya fito.

  • Babban Taron APC: Ƙungiyar Masu Ruwa Da Tsaki Ta Amince Da Yilwatda
  • 2027: Atiku Ya Gargaɗi Magoya Bayansa Kan Tsangwamar Jama’ar Peter Obi

Duk da haka, rahotanni na baya-bayan nan sun nuna cewa gwamnatin Shugaba Donald Trump ta Amurka ta yi imani cewa ƙasar na buƙatar alamar haɗin kai na addini ba kawai a yankin yamma maso kudu ba, har ma a kowai vangare na ƙasar.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Ko da yake wata majiya a arewa ta ce Amurka na iya neman daidaito na addini don voye ainihin manufofinta a Nijeriya, an gano cewa shugabannin siyasa na arewa san yi watsi da tattaunawar tare da cikakken bincike ba.

Daga cikin sunayen Kiristoci uku da suka fito kwanan nan a matsayin yiwuwar ‘yan takara don daidaiton addini, an samu labarin cewa masu ruwa da tsaki a arewa sun yi watsi da yiwuwar takarar Bishop Kukah, yayin da wasu masana a arewa suka ce an sanya masa laƙabi da yana cikin siyasa sosai.

An ruwaito cewa ba saboda ya tava riƙe mukamin siyasa ba ne aka kawo wannan lamari, amma wani bayani ne kan rawar da ya taka a kwamitin zaman lafiya na ƙasa da kuma yadda yake bayyana ra’ayinsa kan al’amuran ƙasa.

Majiyar ta bayyana cewa an riga an ɗauki bishop a matsayin ɗan siyasa kuma sanya shi a muƙamin siyasa na iya rage gudunmawarsa ga ƙasa.

Bayan wannan mataki na Amurka da aka ambata, an tattara cewa wasu sunaye ban da na Bishop Kukah an yi nazari a kansu ga jiga-jigan siyasa a arewa. Sunayen sun haɗa da ministan tsaro, Janar Christopher Musa, da kuma shugaban jam’iyyar APC, Farfesa Nentawe Yilwatda.

Wani majiya ta ce, “Bishop Kukah na iya kasa yin aiki yadda ya kamata, saboda wasu masu sharhi suna ganin shi a matsayi mai tuzarta siyasa kuma hakan ya fi faruwa saboda rawar da ya taka a rayuwarsa zuwa yanzu. Janar Musa ba a bayyana shi haka ba. Ya yi aikin sojoji, kuma yanzu shi minista ne.

“An haife shi a Jihar Sakwato kuma ba a gan shi a matsayin mutum mai matsala. Yayi da shi kuma Farfesa Yilwatda ya kasace kammalallen mutum. Kwanaki kaɗan da ya bayyana a fagen siyasa, amma kamar Musa, bai yi fice a vangare siyasa ba.”

An bayyana cewa ko kafin sabon yunƙuri na daidaita addini a ofishin shugaban ƙasa, tun wasu watanni da suka gabata ƴan arewa sun riga sun fara dubawa a cikin ‘yan takarar da ake sa ran za a ba da shawarar su maye gurbin mataimakin shugaban ƙasa.

Idan za a iya tunawa dai, batun rabuwar takara tsakanin Tinubu da Shettima a 2027 ya kasance a kan tebur fiye da shekara guda da ta wuce. Aƙalla sunaye shida ne suka fara bayyana a tattaunawar maye gurbin Shettima, kafin a sami sabon matsin lamba daga Amurka.

Majiyoyi sun ce wasu shugabanni a faɗin ƙasar ma suna nazarin yiwuwar daidaito na addini a cikin majalisar Tinubu don rage irin tashin hankali da aka ƙirƙiro kafin zaven 2023.

Wasu daga cikin sunayen da suka bayyana sun haɗa da tsohon shugaban jam’iyyar APC, Dakta Umar Abdullahi Ganduje da tsohon gwamnan Jihar Zamfara, Sanata Abdulaziz Yari, da tsohon gwamnan Jihar Kano kuma shugaban jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwakwanso.

Sauran sun haɗa da shugaban majalisar wakilai, Hon Tajudeen Abbas da tsohon shugaban majalisar wakilai, Yakubu Dogara, da mashawarci na tsaron ƙasa, Malam Nuhu Ribadu.

Sai dai an samu labari cewa ƙungiyar masu nazarin siyasa tana da ra’ayin cewa idan shugaban ƙasa na son naɗa Kirista a matsayin wanda zai maye gurbin Shettima, ya zavi Dogara, yayin da sauran ‘yan takara ma an bincika su wajen sanin ƙarfinsu da rauninsu.

Saoda haka, tun bayan da Amurka ta bayyana daidaito na addini kafin zaven 2027, ya bambanta bincike da matakin tattaunawa, in ji wata majiya a ƙarshen mako.

2027
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
Siyasa

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Next Post
APC Ta Musanta Bai Wa Gwamnonin Da Suka Sauya Sheƙa Tikitin Takara Na Kai Tsaye A 2027

APC Ta Musanta Bai Wa Gwamnonin Da Suka Sauya Sheƙa Tikitin Takara Na Kai Tsaye A 2027

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.