ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Ana Zazzafar Muhawara Kan Muslim-muslim Tiket A Takarar Tinubu

by Leadership Hausa
5 months ago
2027

Masu tsara dabarun siyasa na arewa da ra’ayoyin shugabannin sun cire yiwuwar ɗaukar Bishop Mathew Hassan Kukah, a matsayin mai yiwuwa ya maye gurbin mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima a zaven 2027.

Wani yunƙuri na baya-bayan nan, wanda ake cewa Amurka ta tayar, ya tayar da zazzafar da muhawara game da tikitin Musulmi-Musulmi da Shugaba ƙasa, Bola Tinubu ya yi amfani da shi a zaven 2023.

Shugaba Tinubu ya yi takara da Sanata Shettima a cikin tsarin Musulmi-Musulmi tiket, wanda wasu shugabannin Kiristoci a ƙasar suka yi adawa da shi.

ADVERTISEMENT

Amma adawar ta ɗan ragu bayan manyan kamfen-kamfen da suka jaddada halayen Tinubu na juriya ga addini da kuma zaman lafiya na addinai da ke akwai a yamma maso kudu, inda ya fito.

  • Babban Taron APC: Ƙungiyar Masu Ruwa Da Tsaki Ta Amince Da Yilwatda
  • 2027: Atiku Ya Gargaɗi Magoya Bayansa Kan Tsangwamar Jama’ar Peter Obi

Duk da haka, rahotanni na baya-bayan nan sun nuna cewa gwamnatin Shugaba Donald Trump ta Amurka ta yi imani cewa ƙasar na buƙatar alamar haɗin kai na addini ba kawai a yankin yamma maso kudu ba, har ma a kowai vangare na ƙasar.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Ko da yake wata majiya a arewa ta ce Amurka na iya neman daidaito na addini don voye ainihin manufofinta a Nijeriya, an gano cewa shugabannin siyasa na arewa san yi watsi da tattaunawar tare da cikakken bincike ba.

Daga cikin sunayen Kiristoci uku da suka fito kwanan nan a matsayin yiwuwar ‘yan takara don daidaiton addini, an samu labarin cewa masu ruwa da tsaki a arewa sun yi watsi da yiwuwar takarar Bishop Kukah, yayin da wasu masana a arewa suka ce an sanya masa laƙabi da yana cikin siyasa sosai.

An ruwaito cewa ba saboda ya tava riƙe mukamin siyasa ba ne aka kawo wannan lamari, amma wani bayani ne kan rawar da ya taka a kwamitin zaman lafiya na ƙasa da kuma yadda yake bayyana ra’ayinsa kan al’amuran ƙasa.

Majiyar ta bayyana cewa an riga an ɗauki bishop a matsayin ɗan siyasa kuma sanya shi a muƙamin siyasa na iya rage gudunmawarsa ga ƙasa.

Bayan wannan mataki na Amurka da aka ambata, an tattara cewa wasu sunaye ban da na Bishop Kukah an yi nazari a kansu ga jiga-jigan siyasa a arewa. Sunayen sun haɗa da ministan tsaro, Janar Christopher Musa, da kuma shugaban jam’iyyar APC, Farfesa Nentawe Yilwatda.

Wani majiya ta ce, “Bishop Kukah na iya kasa yin aiki yadda ya kamata, saboda wasu masu sharhi suna ganin shi a matsayi mai tuzarta siyasa kuma hakan ya fi faruwa saboda rawar da ya taka a rayuwarsa zuwa yanzu. Janar Musa ba a bayyana shi haka ba. Ya yi aikin sojoji, kuma yanzu shi minista ne.

“An haife shi a Jihar Sakwato kuma ba a gan shi a matsayin mutum mai matsala. Yayi da shi kuma Farfesa Yilwatda ya kasace kammalallen mutum. Kwanaki kaɗan da ya bayyana a fagen siyasa, amma kamar Musa, bai yi fice a vangare siyasa ba.”

An bayyana cewa ko kafin sabon yunƙuri na daidaita addini a ofishin shugaban ƙasa, tun wasu watanni da suka gabata ƴan arewa sun riga sun fara dubawa a cikin ‘yan takarar da ake sa ran za a ba da shawarar su maye gurbin mataimakin shugaban ƙasa.

Idan za a iya tunawa dai, batun rabuwar takara tsakanin Tinubu da Shettima a 2027 ya kasance a kan tebur fiye da shekara guda da ta wuce. Aƙalla sunaye shida ne suka fara bayyana a tattaunawar maye gurbin Shettima, kafin a sami sabon matsin lamba daga Amurka.

Majiyoyi sun ce wasu shugabanni a faɗin ƙasar ma suna nazarin yiwuwar daidaito na addini a cikin majalisar Tinubu don rage irin tashin hankali da aka ƙirƙiro kafin zaven 2023.

Wasu daga cikin sunayen da suka bayyana sun haɗa da tsohon shugaban jam’iyyar APC, Dakta Umar Abdullahi Ganduje da tsohon gwamnan Jihar Zamfara, Sanata Abdulaziz Yari, da tsohon gwamnan Jihar Kano kuma shugaban jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwakwanso.

Sauran sun haɗa da shugaban majalisar wakilai, Hon Tajudeen Abbas da tsohon shugaban majalisar wakilai, Yakubu Dogara, da mashawarci na tsaron ƙasa, Malam Nuhu Ribadu.

Sai dai an samu labari cewa ƙungiyar masu nazarin siyasa tana da ra’ayin cewa idan shugaban ƙasa na son naɗa Kirista a matsayin wanda zai maye gurbin Shettima, ya zavi Dogara, yayin da sauran ‘yan takara ma an bincika su wajen sanin ƙarfinsu da rauninsu.

Saoda haka, tun bayan da Amurka ta bayyana daidaito na addini kafin zaven 2027, ya bambanta bincike da matakin tattaunawa, in ji wata majiya a ƙarshen mako.

2027
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
APC Ta Musanta Bai Wa Gwamnonin Da Suka Sauya Sheƙa Tikitin Takara Na Kai Tsaye A 2027

APC Ta Musanta Bai Wa Gwamnonin Da Suka Sauya Sheƙa Tikitin Takara Na Kai Tsaye A 2027

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.