ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Ta Musanta Bai Wa Gwamnonin Da Suka Sauya Sheƙa Tikitin Takara Na Kai Tsaye A 2027

by Leadership Hausa
5 months ago
APC

Manyan shugabannin jam’iyyar APC sun yi watsi da bayar da tikitin kai tsaye ga gwamnonin jihohi da suka sauya sheƙa, ciki har da Gwamnan Jihar Akwa Ibom, Umo Eno, Gwamnan Jihar Taraba, Agbu Kefas, da Gwamnan Jihar Ribas, Siminalayi Fubara, waɗanda suka shiga jam’iyyar kwanan nan, haka kuma Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, wanda ake sa ran zai shiga nan ba da jimawa ba.

Wani mamba na kwamitin gudanarwa na APC, wanda ya yi magana ba tare da ya bayyana sunansa ba saboda bai samu izinin yin tsokaci kan batun ba, ya bayyana cewa komawa daga wata jam’iyyar siyasa zuwa APC ba ya tabbatar da samun tikitin kai tsaye.

  • Bayan Ganawa Da Tinubu, Gwamna Abba Zai Iya Komawa APC A Talata Ko Laraba 
  • Tinubu Ya Saita Wa Gwamna Yusuf Hanyar Sauya Sheƙa Zuwa APC

A bisa goyon bayan wannan matsayi, Daraktan yaɗa labarai na APC, Bala Ibrahim, a wata hira ta musamman da manema labarai, ya bayyana APC a matsayin jam’iyyar da dimokuraɗiyya da ci gaba, yana jaddada cewa za a ba dukkan mambobi damar yin takara ba tare da hana wasu ba.

ADVERTISEMENT

Daga cikin gwamnonin PDP da suka koma APC akwai Umo Eno na Jihar Akwa Ibom da Sheriff Oborevwori na Jihar Delta da Peter Mbah na Jihar Inugu da Agbu Kefas na Jihar Taraba da kuma Siminalayi Fubara na Jihar Ribas.

Shugabancin APC a Jihar Kano sun nuna cewa sauya sheƙar gwamnan jihar na gab da faruwa.

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Bayan gwamnonin, wasu fitattun ‘yan siyasa da dama ciki har da ‘yan majalisar tarayya da na jihohi da kuma tsoffin gwamnonin da tsoffin ministoci da sauran shugabannin jam’iyya suma sun bar PDP zuwa APC.

Ko da yake masu sauya sheƙar sun bayar da dalilai daban-daban na shiga jam’iyyar mulki, wasu ‘yan Nijeriya na cewa gaskiyar dalilin shi ne samun sake zaven su zuwa muƙaman da suke kai.

A cikin martaninsa, wani mamba na kwamitin gudanarwa na jam’iyyar APC ya ce canje-canjen sun samo asali ne daga nasarorin Shugaba Bola Tinubu, inda ya ya ce a ƙarshe dai mutane ne za su yanke hukunci na sake zavensa.

APC
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Next Post
Me Ya Sa “Tattaunawa Da Sin” Ta Kasance Ra’ayin Bai Daya Na Kasa Da Kasa

Me Ya Sa “Tattaunawa Da Sin” Ta Kasance Ra’ayin Bai Daya Na Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.