Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana mataimakinsa, Kashim Shettima a matsayin “abokin tafiya na kwarai, wajen samun ci gaba.”
Ya kuma jaddada aniyar gwamnatinsa, na fatattakar ta’addanci da ‘yan bindiga, wadanda a cewarsa; ba za su amince da su ba, sannan kuma ayyukansu na ta’addanci, ya saba wa al’adu da kimar Nijeriya.
- Manoma Da Makiyaya Sun Kulla Yarjejeniyar Zaman Lafiya A Filato
- Kotu Ta Yanke Wa Jarumar Kannywood Samha Hukuncin Ɗaurin Wata 6 A Gidan Yari
Tinubu ya bayyana hakan ne, a lokacin da yake bayyana bude taron majalisar tattalin arzikin kasa, a dakin taro na fadar gwamnati da ke Abuja a ranar Litinin da ta gabata.
A lokacin da yake gabatar da manyan mutane, ya kira Shettima a matsayin “Mai girma mataimakin shugaban kasa, kuma shugaban majalisar tattalin arziki na kasa, Kashim Shettima, abokin tafiya na gari,” daga nan kuma sai ya gabatar da gwamnoni, ministoci da sauran manyan jami’an gwamnati da shugabannin kamfanoni masu zaman kansu da suka halarci taron.
Da yake komawa kan jawabinsa, shugaban ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya sabbin yunkurin karfafa jami’an tsaro da kuma dawo da zaman lafiya a cikin al’ummomin da abin ya shafa.
Ya kuma bayyana shirin kaddamar da shiyyoyin injiniyoyi guda bakwai, domin bunkasa ayyukan noma.
Haka zalika, ya bayyana rashin tsaro a matsayin wani babban tabarbarewar tattalin arziki tare da jaddada bukatar hada karfi da karfe, domin shawo kan lamarin.
Da yake maraba da mahalarta taron na kwanaki biyu, shugaban ya ce; taron ya nuna aniyar ci gaban kasa baki-daya.
Da yake yin karin haske kan nasarorin da gwamnatinsa ta samu, Tinubu ya ce; sauye-sauyen da ake samu ta fuskar tattalin arziki, sun taimaka wajen daidaita tattalin arzikin kasar tare da dawo da kwarin gwiwa a idon duniya.
Ya kara da cewa, samar da ababen more rayuwa a harkokin sufuri, wutar lantarki, bunkasa harkokin sadarwa, gidaje da sauransu, sun kasance abubuwan da aka fi bai wa fifiko.
Haka zalika, Mataimakin Shugaban Kasa Shettima, ya yi kira da a kara zurfafa hadin gwiwa a tsakanin bangarorin gwamnati guda uku, yana mai bayyana majalisar zartarwa a matsayin wani muhimmin bangare na tsara alkiblar tattalin arzikin Nijeriya, ta hanyar fahimtar juna. Sannan, ya bukaci mambobin, da su ba da fifiko wajen rage talauci da samar da ayyukan yi a tsakanin matasa.















Discussion about this post