ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Sake Tunani Game Da Karin Kudin Makaranta A Nijeriya

by Leadership Hausa
3 years ago
Makaranta

Kwanakin baya shugaban Kwalejin Gwamnatin Tarayya da ke Maiduguri, Malam Umar Habeeb Jibril, ya bayyana cewa, dalibai 2 ne daga cikin dalibai 89 da suka samu gurbin karatu a kwalejin suka yi rajista, sauran sun kaurace saboda karin kudin makaranta da aka yi. Makarantar da ya kamata a ce ta dauki dalibai 200 amma sai ta dauki 89 kuma daga cikinsu mutum biyu ne suka zo don yin rajista, a matsayin sabbin dalibai.

Shawarar gwamnatin tarayya na kara kudin makaranta daga Naira 45,000 zuwa Naira 100,000 ya sa dole iyaye suka janye yaransu daga makarantun saboda yadda suke fuskantar radadin matsalar tattalin arziki wanda da al’umma ke fuskanta a fadin kasar nan a halin yanzu.

  • Zamu Sabanta Dakin Karatu Na Sashen Harsunan Nijeriya Na Jami’ar Bayero — Hassan Baita
  • Sin Ta Yi Kira Da A Hada Kai Wajen Samar Da Tsaron Fasahar AI 

Wannan lamarin a ra’ayinmu zai kara ta’azzara matsalar da ake fuskanta a makaratunmu na rashin yara masu zuwa makaranta, zai kuma kara yawan yara masu gararamba a titunan kasar nan ba tare da zuwa makaranta ba.

ADVERTISEMENT

Kididdiga daga Hukumar Kula da Ilimi, Kimiyya da Al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ta nuna cewa akwai fiye da yara miliyan 20 da ba sa zuwa makaranta a Nijeriya.

A kan haka ne, yana da wahalar gaske a iya fahimtar dalilin da ya sa gwamnati ta kara kudin makaranta da kuma yekuwar da take yi na rage yara da ke gararamba a tituna ba sa zuwa makaranta. Wannan shawarar karin kudin makaranta, mataki ne na hana iyaye daga tura yaransu makaranta, musamman ma talakawa da masu gwagwarmayar neman yadda za su samu abin kaiwa bakin salati, abin takaicin ma shi ne makaratun gwamnati sun fi karfin ‘yan Nijeriya talakawa ballantana makarantu masu zaman kansu.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Wani karin abin takaici a nan shi ne, a yankin arewa maso gabas, wanda ya hada da Jihar Yobe, Taraba, Bauchi, Gombe Adamawa da Borno, an kiyasta cewa, kashi 33 cikin 100 na yaran yankin ba sa zuwa makaranta, wanna shi ne mafi yawa a kasar gaba daya, a yankin arewa ta tsakiya kuma akwai kashi 26, Arewa ta yamma akwai kashi 25; kudu maso kudu kuma kashi 24; kudu maso yamma kashi 22 yayin da kuma kudu maso gabas ake da yara kashi 19 da ba sa zuwa makaranta.

Da yawa daga cikin wadannan ‘ya’ya suna gararamba a kan titunan kasar nan inda daga karshe suna zama ‘yan bangar siyasa, wani abin tashin hankali kuma shi ne yadda wasu yaran ke zama abin da wasu bata gari ke amfani da su wajen gudanar da tsaface-tsaface ko kuma su zama makamin da ‘yan ta’adda ke amfani da su wajen aikata ayyukansu na tarzoma a kasa.

Babu tantama, shawarar gwamnati ta kara kudin makaranta a daidai wannan lokacin da ake fuskantar matsalar tattalin arziki ce ta tilasta wa wasu gidaje rage abincin da suke ci a rana, wanda kuma wannan a ra’ayinmu yana nuna yadda gwamnati ba ta dauki harkar ilimi da muhimmancin da ya kamata ba.

Bayanin da ya fito daga shugaban makaranta, Jibril, ya fayyace laifin gwamnatin tarayya karara wadda ya kamata a ce tana kokarin ganin tana karfafa matakin rage yaran da ba su zuwa makaranta a fadin kasar, yana kuma nuna cewa, gwamnati ba da gaske take yi ba na cimma manufofin da suka sa aka kafa makarantun tun da farko.

Idan za a iya tunawa an kafa makarantun hadin kan kasa ‘Unity School’ ne don samar da wani dandamali da zai hada kan ‘yan kasa da kuma gina kasa, an kuma tabbatar da za a iya cimma wannan burin ne ta hanyar samar wa da yara yanayin da za su zauna a wuri daya, su yi karatu a wuri daya, ta yadda hakan zai samar da fahimtar juna a tsakaninsu.

Yana kuma da muhimmanci a fahimmaci cewa, an kafa kwalejojin gwamnatin tarayya na farko ne a shekarar 1964 a a garuruwan Sakkwato (Arewa); Okposi (yankin Kudancin kasar nan) da kuma Warri a yankiin kudu ta tsakiya.

Daga baya aka kafa wasu makarantun don cika burin gwamnatin tarayya na hada kan kasa. Amma kuma abin takaici, a ‘yan shekaru nan aka bar makarantun suka lalace saboda rashin kudaden gudanarwa da kuma rashin sa ido daga bangaren gwamnati.

Kafin ma a yi wannan karin kudin makarantar wanda a halin yanzu ya sa makarantar ta fi karfin talaka, an dade ana tunanin yadda gawmnati ta yi sako-sako da kudurinta na daukar nauyin gudanar da makarantun saboda yadda aka fuskanci karancin kudin gudanarwa da kuma sa ido daga gwamnatin.

Kamar dai sauran ‘Yan Nijeriya, mun damu da rahoton da ke fitowa daga kwalejin gwamnati na Maiduguri, babban birnin Jihar Borno, cibiyar kungiyar Boko Haram da ake kyamar karatun boko.

Ya kamata gwamnati ta dauki matakin gaggwa na rage kudin makarantaun kwalejin gwamnatin tarayya don a samu karin yara masu shiga makarantar musamman ganin yadda ake kokarin cike gibin yaran da ba su zuwa makaranta. Babu wani dalilin yin wannan karin, musamman ganin yadda karin ya haifar da raguwar yara masu shiga makaranta a daidai lokacin da gwamnatin ke so a samu karin yara masu zuwa makaranta, ya zama dole a sake shawara.

Abin takaici ne a ce an bullo da wata manufar gwamnati da ta hana yara zuwa makaranta, musamman a yankin da ‘yan ta’adda ke takura al’umma daga shiga makarantun boko kuma ake da yara masu yawa da ba su zuwa makaranta.

Ra’ayinmu a nan shi ne, ya kamata a ce gwamnatoci a dukkan matakai su dauki nauyin karfafa hanyoyi shigar da yara makaranta da tabbatar da suna ci gaba da karatun tare da kammala karatun a matakin firamare, sakandire kamar dai yadda dokar bayar da ilimi kyauta ta tanada a kundin tsarin mulkin kasar nan.

Makaranta
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Siyasar Ubangida: Baya Ta Haihu A Jihar Ribas

Siyasar Ubangida: Baya Ta Haihu A Jihar Ribas

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.