Tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, ya soki tsohon Ministan Shari’a (AGF), Abubakar Malami, yana mai zarginsa da kutsa fara yi masa shari’ar tuhumarsa kan cin hanci, inda ya ce yanzu al’amura sun juya kan Malami da ke fuskantar irin zarge-zargen.
Lamido ya bayyana hakan ne a wata hira, inda ya tuna yadda aka fara tuhumarsa a zamanin tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, lokacin da Malami ke riƙe da muƙamin ministan shari’a. Ya ce, “Shi ne a fara shari’ata, an kira ni ɓarawo a wancan lokaci, amma yau ga irin kadarorin da ake zarginsa da mallaka.”
- Yadda Masu Kwace Suka Yanke Wa Malamin Makaranta Hannu A Kano
- Sharuɗɗan Da Sule Lamido Ya Gindaya Wa Jam’iyyar PDP A Wa’adin Kwana 10
Ya ce ya tsaya tsayin daka a lokacin shari’ar sa, yana mai cewa amincewa da gaskiya ce ta ba shi ƙwarin gwuiwar fuskantar kotu ba tare da tsoro ba. Haka kuma ya musanta zargin cewa yana ƙoƙarin kusantar gwamnatin Bola Ahmed Tinubu domin kauce wa tuhuma.
A ɓangaren Malami, ana ci gaba da shari’a a kan sa a kotunan tarayya da ke Abuja kan zarge-zargen da suka haɗa da almundahanar kuɗaɗe, da tallafawa ta’addanci da kuma mallakar makamai ba bisa ƙa’ida ba, da zarge-zargen da EFCC da DSS suka shigar.
Ana zargin shi da amfani da kamfanoni wajen ɓoye asalin kuɗaɗen da aka sayi kadarori da su, yayin da shi da matarsa da ɗansa suka samu beli na Naira miliyan 500 kowannensu, yayin da ake ci gaba da sauraron ƙarar a kotu.















Discussion about this post