Al’ummar karamar hukumar Kauru da ke jihar Kaduna sun yi kira ga gwamnatin jihar Kaduna da ta gaggauta kawo musu dauki kan matsalar rashin tsaro da ke barazanar raba su da muhallansu.
Mazauna yankin, wadanda suka hada da Musulmai da Kirista, sun bayyana cewa ‘yan ta’adda sun mamaye kauyuka sama da 39, inda suka kori jama’a daga gidajensu tare da yin garkuwa da mutane fiye da dubu daya.
- Gwamnatin Tarayya Ta Rage Harajin Shigo Da Shinkafa, Motoci Da Wasu Kaya 127
- Wasu Muhimman Abubuwa Da Ba A Sani Ba Game Da Ƙwaƙwalwa
Da yake magana a madadin al’ummar yankin, mai magana da yawun su, Rabaran Musa Hassan Shadari, ya bayyana haka ne a wani taron manema labarai, inda ya ce al’ummar yankin wadanda galibinsu manoma ne inda yace suna neman agajin gaggawa daga gwamnati domin ceto rayuwarsu da ta iyalansu, tare da taimaka musu su ci gaba da harkokin noma kamar yadda suka saba.
Ya ce hare-haren ‘yan ta’addan sun haddasa rufe masallatai sama da 26 da kuma coci- coci sama da 65 a yankuna daban-daban.
Ya kara da cewa, al’ummar yankin sun biya kudin fansa da ya kai naira miliyan 300 domin kubutar da mutanen da aka yi garkuwa da su a wasu kauyukan yankin.
Shadari, ya yi kira ga gwamnati da ta dauki matakin gaggawa ta hanyar girke sansanonin sojoji a yankunan da abin ya shafa, musamman a wannan lokaci da ake shirin shiga damina, domin bai wa manoma damar komawa gonakinsu cikin tsaro.
A nasu bangaren, wasu daga cikin mazauna yankin da suka hada da Yusuf Mathew da Ibrahim Hore, sun bayyana damuwarsu kan yadda matsalar tsaro ke kara ta’azzara, suna mai cewa rayuwarsu da dukiyoyinsu na cikin hadari.
Sun bukaci hukumomi da su dauki matakan gaggawa domin dawo da zaman lafiya a yankin tare da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.















Discussion about this post